Thursday, December 18
Shadow
Kalli Bidiyo: Ta je Saudiyya tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali har sai ya biya mahaifiyarta kudadenta

Kalli Bidiyo: Ta je Saudiyya tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali har sai ya biya mahaifiyarta kudadenta

Duk Labarai
Wannan matashiyar ta je Saudiyya a dakin Ka'aba tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali. Tace Allah ya hanashi abinda yake so har sai ya biya mahaifiyarta kudin ta dake hannunsa. Saidai da yawa sun bayyana cewa irin wannan addu'a da ta yi bata dace ba. https://www.tiktok.com/@realgudgirl0/video/7554450456676764936?_t=ZS-90BWkcIbgqO&_r=1
Karanta Jadawali: An fitar da bayanin Jihohin da dalibai suka fi karbar bashin karatu na NELFUND na Gwamnatin Tarayya

Karanta Jadawali: An fitar da bayanin Jihohin da dalibai suka fi karbar bashin karatu na NELFUND na Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, an fitar da bayanin jihohin da dalibai suka fi karbar Bashin Karatu na Gwamnatin Tarayya da ake kira da NELFUND. Jihohin sune kamar haka: 1. Borno: 61,3842. Kano: 57,9833. Kaduna: 45,0024. Katsina: 43,6025. Oyo: 33,2236. Bauchi:33,0277. Kwara: 31,6408. Plateau: 31,3149. Gombe: 31,30810. Taraba: 26,505
PENGASSAN ta amince ta janye yajin aiki bayan Dangote ya amince ya mayar da ma’aikata 800 da ya kora bakin aiki

PENGASSAN ta amince ta janye yajin aiki bayan Dangote ya amince ya mayar da ma’aikata 800 da ya kora bakin aiki

Duk Labarai
Ƙungiyar manyan ma'aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya, PENGASSAN ta amince da jingine yajin aikin da shiga bayan samun saɓani da matatar mai ta Dangote Yajin aikin na zuwa ne bayan PENGASSAN ta zargi mattaar da korar fiye da ma'aikata 800 saboda sun nuna sha'awar shiga ƙungiyar. Gwamnatin Najeriya ce ta shiga tsakani a sasancin ɓangarorin biyu da ake yi tun ranar Litinin, to amma sai a yau Laraba ne aka cimma matsaya. Cikin wata sanarwa da ma'aikatar kwadagon ƙasar ta fitar ta ce matatar ta amince da mayar da ma'aikatan da ta kora domin su ci gaba da aiki da ita. "Babu ma'aikacin da zai cutu sakamakon saɓanin matatar Dangote da PENGASSAN," a cewar sanarwar. A nata ɓangare, ƙungiyar ta PENGASSAN ta ''amince ta fara shirye-shiryen janye yajin aikin''. Tun bayan fara...
Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Hassan Make-Up ya bayyana cewa, yana neman Afuwar duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. Ya bayyana hakane yayin da yake kusa da ka'aba yake rokon dan darajar dakin Ka'aban duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. A baya dai an ga Hassan Make-Up har kuka ya rika yi bayan da ya samu zuwa Aikin Umrah. https://www.tiktok.com/@officielhassanmakeup227/video/7555127311583038776?_t=ZS-90A3JHC3sYq&_r=1
Kalli Bidiyo: Nima ga dana da Kachiya aka Haifeshi, Dan haka, Malam Lawal Triumph yayi daidai, Haihuwar mutum da Kachiya ba Karama bace>>Inji Malam Abdulhamid Dahir

Kalli Bidiyo: Nima ga dana da Kachiya aka Haifeshi, Dan haka, Malam Lawal Triumph yayi daidai, Haihuwar mutum da Kachiya ba Karama bace>>Inji Malam Abdulhamid Dahir

Duk Labarai
Malam Abdulhamid Dahir ya goyi bayan Sheikh Lawal Triumph kan kalaman da yayi cewa, Haihuwar mutum da Kachiya ba karama bane. Malam ya bayar da misali da dansa inda yace shima da Kachiya aka haifeshi dan haka, Haihuwar Mutum da Kachiya ba karama bace. Kalli Bidiyonsa a kasa: https://www.tiktok.com/@sheikh_lawan_triumph/video/7555274342100258055?_t=ZS-90A2h8MjRr7&_r=1
Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar PENGASSAN

Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar PENGASSAN

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar rushe kungiyar manyan ma'aikatan man fetur ta PENGASSAN. Yace idan kungiyar ta ci gaba da nuna son kai ba tare da la'akari da abubuwan da zasu kawowa al'umma ci gaba ba, ya kamata Gwamnatin tarayya ta soketa. Ranar Asabat, Kungiyar PENGASSAN ta fara yajin aiki bayan da ta zargi matatar man Dangote da korar membobin ta 800 daga aiki. A bangaren Dangote, yace Wannan yajin aiki PENGASSAN na son yin amfani dashine dan cimma wani buri nata na saka 'yan Najeriya cikin wahala. A hirar da aka yi dashi a Arise TV, Ndume yace baya goyon bayan Ayyukan kungiyoyin kwadago da suke daukar matakan biyan bukatarsu maimakon bukatar al'ummar Najeriya. Yace ina PENGASSAN take a lokacin da aka cire tallafin man fetur a Najeriy...
An tashi baram-baram a zaman sulhu da aka yi yunkurin yi tsakanin kungiyar PENGASSAN da Dangote

An tashi baram-baram a zaman sulhu da aka yi yunkurin yi tsakanin kungiyar PENGASSAN da Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun ce zaman sulhu da aka yi tsakanin wakilan kungiyar PENGASSAN da na Matatar Dangote an tashi ba tare da cimma matsaya ba. Gwamnatin tarayya ce ta kira zaman wanda aka fara ranar Litinin da misalin karfe 4 p.m.. Ministan kwadago, Mohammed Dingyadi da karamar ministan Kwadago, Nkiruka Onyejeocha sun halarci zaman wanda aka shafe awanni 9 ana yi. Minista Dingyadi yace za'a dawo ci gaba da zaman da misalin karfe 2 p.m. na ranar Talata. Gwamnatin tarayya tace tana duba abinda wannan rikici zai jawowa Najeriya ne shiyasa take kokarin sulhunta Bangarorin Dangote da PENGASSAN.
Kalli Bidiyon: An aiko min Sako in daina Karanta Jawahilin Ma’ani>>Inji Malam Lawal Triumph

Kalli Bidiyon: An aiko min Sako in daina Karanta Jawahilin Ma’ani>>Inji Malam Lawal Triumph

Duk Labarai
Bidiyon malam Lawal Triumph inda yake fadin cewa, an aika masa da sako ya daina karanta Jawahiril ma'ani saboda makiya sun yi yawa ya watsu sosai. Malam Lawal Triumph dai a yanzu shine ake ta batunsa a Kano dama kafafen sada zumunta saboda kalaman da basu kamata ba da ake zarginsa da fadi a kan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). https://www.tiktok.com/@sadiq_umar/video/7555431202769980688?_t=ZS-909t5dMQWTQ&_r=1
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta baiwa membobinta umarnin su shirya shiga yajin aiki dan goyawa Kungiyar PENGASSAN baya a fadan da take da Dangote

Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta baiwa membobinta umarnin su shirya shiga yajin aiki dan goyawa Kungiyar PENGASSAN baya a fadan da take da Dangote

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta yi kira ga Membobinta dasu shirya shiga yajin aiki dan giyawa kungiyar PENGASSAN baya game da fadan da take da matatar man fetur din Dangote. Hakan na zuwane bayan yajin aikin da kungiyar PENGASSAN ta fara wanda ya dakatar da ayyuka a matatar man fetur din Dangote. Kotun Masana'antu ta dakatar da kungiyar PENGASSAN shiga yajin aikin a ranar lit, saidai PENGASSAN tace bata samu hakan a hukumance ba daga kotun. A hirarsa da Punchng, shugaban NLC, Joe Ajaero ya bayyana cewa membobinsu su shirya dan fara yajin aikin nuna goyon baya ba kungiyar PENGASSAN inda ya zargi Matatar man fetur din Dangote da samar da tsare-tsaren masu take hakkokin ma'aikata.
Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Kwana daya bayan samun Rahoton cewa, zai fito takarar shugaban kasa, Gwamnatin Tarayya ta fara sukar Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan

Duk Labarai
Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na da ‘yancin tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekarar 2027. Sai dai ta jaddada cewa ‘yan Najeriya ne za su yi masa hukunci saboda ba su manta 'munin' mulkin Jonathan ba, ta kuma kwatanta mulkin Tinubu da abin da ta bayyana a matsayin “gagarumin ci gaban tattalin arziƙi” Fadar shugaban ƙasar ta kuma ɗora alhakin fara yaƙin neman zaɓe da wuri kan masu neman kifar da shugaba mai ci. Hakan na zuwa ne a rana guda da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba za ta bai wa Jonathan tikitin tsayawa takara kai tsaye ba, inda ta bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin “zaɓuɓɓukan da take dubawa.