Monday, March 16
Shadow
Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Kalli Bidiyon yanda jami’in tsaron Civil Defence ke tonawa wani na hannun daman Gwamna Asiri cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake hana mutane zàmàn Lafiya

Duk Labarai
Wannan wani jami'in Hukumar Civil Defence ne a jihar Imo da ya bayyana wani me suna, Chinasa Nwaneri da cewa shine ke daukar nauyin Tshàgyèràn dake aikata ayyukan Ashsha na hare-hare a jihar. Chinasa Nwaneri daya ne daga cikin masu taimakawa gwamnan jihar Imo na musamman akan ayyukansa. Wannan zargi dai yayi nauyi inda mutane ke cewa ya kamata a bincikeshi. https://twitter.com/General_Somto/status/1996841460642308532?t=d9ydlNYqHeWR7BwvdL3Ujg&s=19
Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Allah Sarki, Kalli Bidiyon yanda wani dan Najeriya ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta saboda murnar shugaba Tinubu ya nada janar Christopher Musa Ministan tsaro

Duk Labarai
Wannan wani matashi dan Najeriya ne da yace yana tsaka ds tafiya zuwa wani gari amma da yaji labarin an baiwa Janar Christopher Musa mukamin Ministan tsaro. Shine ya tsaya a wani kauye ya sayi Buhun shinkafa ya rabawa mutane kyauta. Yayi fatan cewa Allah ya baiwa sabon Ministan nasara ya kawo karshen matsalar tsaron Najeriya. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1996917787412025722?t=PFhCXZrlhsAi_5EPBBrEGA&s=19
Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Wata Sabuwa: Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno sun bude gidan Rediyo suna yada shirye-shiryensu da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Borno na cewa kungiyar dake ikirarin Jihadi ta ÌŚWÀP ta fadada ayyukan gidan rediyonta inda take yada shirye-shiryenta da yarukan Hausa, Kanuri, da Turanci. Saidaj ba kaitsaye gidan Rediyon ke aiki ba, suna dauka ne sai a rika turawa kamar yanda ake tura waka ko fim, kamar yanda masanin harkar tsaro, BrantPhilip ya ruwaito. Ya kuma wallafa Sautin muryar daya daga cikin shirye-shiryen kungiyar da aka nada wanda aka yadashi da Turanci. https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1996857715600007465?t=XK7ddJaXBlEmU-7-7FOPsg&s=19 Wannan lamari dai ya zowa mutane da mamaki inda da yawa suka rika tunanin yaushe Kungiyar har ta samu nutsuwar yin abubuwa haka?
Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Kalli karin Bidiyon giwayen da suka bayyana a jihar Borno

Duk Labarai
A jiyane dai muka samu Rahoton cewa, Giwaye sun bayyana garin Kala Balge na jihar Borno inda mutane suka taru suna kallonsu. Zagazola Makama yace giwayen sun rika cinye amfanin gona inda yayi kira ga mahukunta dasu kaiwa jama'a dauki. Bidiyon da hotunan giwayen sun ci gaba da yaduwa a kafafen sada zumunta Wasu rahotanni sun ce giwayen sun shiga garin ne daga kasar Chadi. https://www.tiktok.com/@umarfaruq6966/video/7579953257259339029?_t=ZS-91y7VEZ0NGa&_r=1
Ji Abinda ya faru da shafukan sada zumunta na Hadiza Gabon bayan da Masoya Adam A. Zango suka sha Alwashin yin Unfollow dinta

Ji Abinda ya faru da shafukan sada zumunta na Hadiza Gabon bayan da Masoya Adam A. Zango suka sha Alwashin yin Unfollow dinta

Duk Labarai
Bayan da Hadiza Gabon ta ki saka hoton Adam A. Zango a dakin da take hira da mutane wanda ya jawo cece-kuce sosai. Daya daga cikin matakan da masoya Adam A. Zango suka sha alwashin dauka shine zasu yi Unfollow dinta a shafukan sada zumunta dan nuna bacin Ransu. Tun bayan shan wannan Alwashi yanzu sama da awanni 24 kenan Hutudole yana saka ido akan shafukan na sada zumuntar Hadiza Gabon dan ganin ko zata samu raguwar mabiya. Mutane musamman a kasashen Turawa sukan dauki irin wannan mataki na Unfollow ga wani da yayi wani abinda basa so. Saidai Hutudole har zuwa yanzu ya lura cewa Hadiza Gabon bata rasa mabiya ba ko kuma mabiyanta basu ragu ba a shafukanta na sada zumunta.
‘Yan majalisar jihar Rivers 16 sun bar PDP zuwa APC

‘Yan majalisar jihar Rivers 16 sun bar PDP zuwa APC

Duk Labarai
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Rivers, Martin Amaewhule, ya sauya sheƙa tare da wasu ƙarin mambobi 15 na majalisar a ranar Juma’a, lamarin da ya ƙara dagula harkokin siyasar jihar wadda ke fama da rikice-rikicen cikin gida tun watanni da dama. Rahotanni sun nuna cewa sauya sheƙar na da alaƙa da rikicin siyasa da ya dabaibaye jihar. Wannan mataki ya mayar da adadin mambobin majalisar da suka koma jam’iyyar APC zuwa 16 gaba ɗaya. Sauya sheƙar ya faru ne a wani zama na musamman da majalisar ta yi inda mambobin suka bayyana cewa sun yanke shawarar komawa APC
Kalli Bidiyon: Idan Kana da mata, zaka kara aure ka zo neman diyata, na gano kana zama a teburin Meshayi, Ba zan baka diyata ba dan kai ba adali bane>>Inji Malam

Kalli Bidiyon: Idan Kana da mata, zaka kara aure ka zo neman diyata, na gano kana zama a teburin Meshayi, Ba zan baka diyata ba dan kai ba adali bane>>Inji Malam

Duk Labarai
Wannan malamin ya bayyana cewa idan mutum na da mata kuma yana neman kara aure ya je neman diyarsa kuma ya gano mutum na cin Indomie a teburin me shayi to ba zai bashi diyarsa ba. Yace dalili kuwa shine hakan ba adalci bane. Ka bar iyalinsa a gida da garau-garau ka je Teburin me shayi cin Indomie. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7580089084819868940?_t=ZS-91xuxXVejnV&_r=1
Kalli Bidiyon: Shi Abu idan dan Allah aka yishi menene na Nunawa Duniya? Amma idan dan Allah yayi Allah ya bashi lada>>Inji Babban Yaron Nazir Ahmad Sarkin Waka, Abba C Sale game da gina masallacin da Rarara yayi

Kalli Bidiyon: Shi Abu idan dan Allah aka yishi menene na Nunawa Duniya? Amma idan dan Allah yayi Allah ya bashi lada>>Inji Babban Yaron Nazir Ahmad Sarkin Waka, Abba C Sale game da gina masallacin da Rarara yayi

Duk Labarai
Babban yaron Naziru Ahmad Sarkin Waka, Abba C Sale ya bayyana cewa idan Dauda Kahutu Rarara dan Allah ya gina masallacinsa ba sai ya nunawa Duniya ba. Amma duk da haka yace yana fatan Allah ya bayar da lada idan dan Allah yayi. Ya bayyana hakane a Bidiyon daya saki a Tiktok. https://www.tiktok.com/@abbacsale2/video/7580282459506461973?_t=ZS-91xqFHoRhxZ&_r=1 A yaune dai Dauda Kahutu Rarara zai bude katafaren masallacin da ya gina a mahaifarsa dake Kahutu.