Thursday, December 18
Shadow
Kalli Bidiyon: Muna muna kan Kalaman Sheikh Lawal Triumph kuma nasan cewa, a cikin Mintuna 10 zai kawo hujjojin kalaman da yayi>>Inji Sheikh Sani Rijiyar Lemu

Kalli Bidiyon: Muna muna kan Kalaman Sheikh Lawal Triumph kuma nasan cewa, a cikin Mintuna 10 zai kawo hujjojin kalaman da yayi>>Inji Sheikh Sani Rijiyar Lemu

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Sani Rijiyar Lemu ya bayyana goyon baya ga Malam Lawal Triumph game da zargin da ake masa na yiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Batanci. Sheikh Sani yace Kalaman da malam yayi suna tare dashi suma akan irin wannan fatawar suke. Yace da ake cewa wai idan ba'a kama Lawal Triumph ba, shima Abduljabbar a sakeshi, yace idan so suke a saki Abduljabbar su fito kawai su fada ba sai sun yiwa wani sharri ba. https://www.tiktok.com/@tijjanihassangwale/video/7554523563399580946?_t=ZS-906OnuDGFDV&_r=1
Kalli Bidiyo: Ku Jahilai Masu cewa wai ni mawakine in daina saka baki wajan kare Annabi, ku je ku tambayi malamanku irin gudummawar da mawaka suka bayar wajan kare Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Tijjani Gandu

Kalli Bidiyo: Ku Jahilai Masu cewa wai ni mawakine in daina saka baki wajan kare Annabi, ku je ku tambayi malamanku irin gudummawar da mawaka suka bayar wajan kare Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)>>Inji Tijjani Gandu

Duk Labarai
Shahararren mawakin siyasa, Tijjani Gandu ya bayyana goyon bayan kamawa da hukunta Malam Lawal Triumph kan zargin yiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Batanci. Yace su suna kare Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) a yayinda dayen bangaren kuma suna kare dan kungiyane. Yace kuma masu zaginsa cewa, wai shi mawaki ne Jahilaine, su je su tambayi irin gudummawar da mawaka suka bayar wajan kare Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) musamman idan za'a je yaki. https://www.tiktok.com/@tijjanigandu/video/7554170949399072008?_t=ZS-906Km3PSuBd&_r=1
Kungiyar Manyan ma’aikatan Man fetur, PENGASSAN ta baiwa membobinta umarnin dakatar da aikawa matatar Man Fetur ta Dangote Danyen Mai da Gas, Dangoten ya koka

Kungiyar Manyan ma’aikatan Man fetur, PENGASSAN ta baiwa membobinta umarnin dakatar da aikawa matatar Man Fetur ta Dangote Danyen Mai da Gas, Dangoten ya koka

Duk Labarai
Rahotanni sun ce kungiyar manyan ma'aikatan man fetur, PENGASSAN sun baiwa membobinsu umarnin su dakatar da aikawa matatar man fetur ta Dangote Danyen Man fetur da Gas. Kungiyar tace ta yi hakanne da gudanar da addu'a da neman Shuwagabannin Najeriya su takawa Dangote birki kan karan tsaye da yake a harkar man fetur a Najeriya. Hakan na zuwane bayan da Matatar Dangote din ta sallami ma'aikatan ta 800 bayan da suka shiga lingo PENGASSAN. PENGASSAN tace Dangote ya dauko indiyawa amma ya kori 'yan Najeriya 800 da suke masa aiki. Tace a yayin da ake biyan injiniyoyi 'yan Najeriya Albashin 385,000 a wata, Indiyawa da Dangote ya dauko yana biyansu albashin dala $5000 ne watau kwatankwacin Naira Miliyan 7.5. Kungiyar PENGASSAN ta bukaci Dangote ya mayar da ma'aikatan 'yan Najeriya...
Kalli Bidiyon yanda Sheikh Dr. Ahmad Gumi ke daurawa dansa da ya gama NDA mukamin 2nd Lieutenant

Kalli Bidiyon yanda Sheikh Dr. Ahmad Gumi ke daurawa dansa da ya gama NDA mukamin 2nd Lieutenant

Duk Labarai
Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya daurawa dansa mukamin 2nd Lieutenant bayan da ya kammala makarantar horas da sojoji ta NDA. A Bidiyon da ya watsu a kafafen sadarwa anga malam yana daurawa dan nasa mukamin inda ake daukarsa hotuna. kalli Bidiyon anan https://x.com/Better_Kaduna/status/1971975841715572941?t=0ldID3p7wJFJq4wxNU-o8w&s=19
Kalli Bidiyon:Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayar da labarin garin da yane aka lakada masa na jaki

Kalli Bidiyon:Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayar da labarin garin da yane aka lakada masa na jaki

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayar da labarin garin da yaje aka masa dukan kawo wuka. Saidai malam yace ya daina fadin garin saboda mutanan garin na cewa yana ja musu zagi da tsinuwa kuma an dade da yin abin. Malam yace dan haka ya daina kiran sunan garin bayan gyaran da aka masa. https://www.tiktok.com/@nurasara531/video/7554842961033432338?_t=ZS-9067c6ypuJl&_r=1
Kalli Bidiyon: Ni a wajena babu Musulmi makiyin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko da wanda basa Maulidi, Basu Fahimceshi bane amma suna da hanyar da suke bi wajan daraja Annabi>>Inji Dr. Murtala Abubakar Argungun

Kalli Bidiyon: Ni a wajena babu Musulmi makiyin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko da wanda basa Maulidi, Basu Fahimceshi bane amma suna da hanyar da suke bi wajan daraja Annabi>>Inji Dr. Murtala Abubakar Argungun

Duk Labarai
Malamin Addinin Musulunci, Dan Darika, Dr. Murtala Abubakar Argungun ya bayyana cewa, shi a wajensa babu Musulmi makiyin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Malam yace ko da wadanda basa Maulidi baya daukarsu a matsayin makiyan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) kawai dai akwai sabanin fahimta ne kan yanda ya kamata a girmama Annabi. Wannan kalamai nasa sun jawo masa yabo sosai inda mutane ke cewa haka ya kamata a rika wa'azi. https://www.tiktok.com/@drmurtalaabubakarargungu/video/7552325369139973394?_t=ZS-9061J3L3XIP&_r=1
Idan Gwamnati ta ki hukunta Lawal Triumph, to bata da hurumin ci gaba da tsare Abdul Jabbar, hakanan idan wani ya taba Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) nan gaba ba za’a iya hukuntashi ba>>Inji Abdullahi Sani Tijjani

Idan Gwamnati ta ki hukunta Lawal Triumph, to bata da hurumin ci gaba da tsare Abdul Jabbar, hakanan idan wani ya taba Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) nan gaba ba za’a iya hukuntashi ba>>Inji Abdullahi Sani Tijjani

Duk Labarai
Malamin Darika, Abdulfatahi Sani Tijjani ya bayyana cewa idan gwamnati ta kyale Sheikh Lawal Triumph bata hukuntashi ba. Yace daliban Abdul Jabbar Zasu fito su nemi a sakeshi kuma Gwamnatin bata da hurumin ci gaba da rikeshi. Hakanan yace wani ba zai taba Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) nan gaba ba a iya hukuntashi ba. https://www.tiktok.com/@shaaweuei5p/video/7554541718335507730?_t=ZS-905UamenI3N&_r=1
Kalli Bidiyon: Mu ‘yan Fim mun fi malaman Wahabiyawa wanda basa ganin Kimar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Ilimi>>Inji Tijjani Faraga

Kalli Bidiyon: Mu ‘yan Fim mun fi malaman Wahabiyawa wanda basa ganin Kimar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Ilimi>>Inji Tijjani Faraga

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Tijjani Faraga ya bayyana cewa su 'yan Kannywood sun barranta kansu da malaman Wahabiyawa da basa ganin kimar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Yace kai su 'yan fim sun fi malaman Wahabiyawa da basa ganin Kimar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ilimi. Kalli Bidiyonsa a kasa:: https://www.tiktok.com/@tijjani.faraga3/video/7554660650505538824?_t=ZS-905RRLIpIMz&_r=1
Da Duminsa: Mun dawo mun ci gaba da sayar da man fetur da kudin Naira>>Inji Matatar man Dangote, kasa da awanni 24 bayan da tace ta dakatar da sayar da man da kudin Naira

Da Duminsa: Mun dawo mun ci gaba da sayar da man fetur da kudin Naira>>Inji Matatar man Dangote, kasa da awanni 24 bayan da tace ta dakatar da sayar da man da kudin Naira

Duk Labarai
Matatar man fetur din Dangote ta sanar da cewa ta dawo ta ci gaba da sayar da man fetur da kudin Naira Hakan na zuwane kasa da awanni 24 bayan da matatar tace ta dakatar da sayar da man fetur din da kudin Naira saboda man data tanada dan sayarwa da kudin Naira ya kare Saidai a sabuwar sanarwar, Matatar Dangote tace ta dawo sayar da man fetur din da kudin Naira bayan shiga tsakani da shugaban kwamitin sayar da man fetur da kudin Naira, Dr. Zacch Adedeji yayi. Matatar tace yanzu duk masu sayen man zasu iya saya da kudin Naira kuma zata kai musu kyauta.