Tuesday, December 16
Shadow
Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa kasashen Turawa yin hutu

Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa kasashen Turawa yin hutu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kama hanyar zuwa kasashen Faransa da Ingila inda zai yi hutu acan. Gwamnan Imo dana Legas da sakataren Gwamnatin tarayya na daga cikin wadanda suka mai rakiya zuwa filin jirgin. Fadar shugaban kasa tace shugaban zai kwashe kwanaki 10 ne yana wannan hutun. https://twitter.com/NTANewsNow/status/1963593117988200540?t=gFM_kzD3OO7721pi9xO8VQ&s=19
Kalli Hotuna yanda ‘yansanda suka kulle ofishin Jam’iyyar ADC a jihar Kaduna suka hana jam’iyyar taro

Kalli Hotuna yanda ‘yansanda suka kulle ofishin Jam’iyyar ADC a jihar Kaduna suka hana jam’iyyar taro

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kaduna sun bayyana cewa, 'yansanda sun kulle ofishin jam'iyyar ADC a jihar yayin da kungiyar ke shirin gudanar da taro. Wasu daga cikin 'yan jam'iyyar sun hau kafafen sada zumunta suna bayyana mamaki da rashin jin dadinsu. ""An Jibge Jami'an Tsaro Sama Da Mota 20 Domin A Hanamu Taron Da Zamuyi Ayau" A Ofishin Jami'iyyar ADC Dake Kan Titin Ali Aƙilu. Wacce irin siyasa akeyi haka a jihar Kaduna?, anata amfani da jami’an tsaron da'aka samar domin tsare ƙimar Demokraɗiyya ana yiwa Demokraɗiyyar fyaɗe. sannan a turo wasu wanda basufi ƙarfin cikinsu ba, wanda da ƙyar suke iya biyan kudin haya, suzo media suna kare ƙarya da zalunci. Ance an kashe adawa a jihar Kaduna, to kenan me ake tsoro tunda an kashe adawa?, Allah ya kyauta" Inji Comrades DanHabu ""An Jibge...
Kungiyar Dattawan Arewa ta bukaci shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa ta bukaci shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a Arewa

Duk Labarai
Ƙungiyar dattawan Arewacin Najeriya (NEF) ta buƙaci shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a yankin sakamakon matsalar tsaro da ke ci gaba da ta'azzara wanda ya lalata rayuka da tattalin arzikin ƙasar. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya fitar, ƙungiyar ta bayyana damuwarta kan hare-hare da garkuwa da mutane da kashe su ba ƙaƙautawa da ake ci gaba da yi a yankin. Ya yi gargaɗin cewa idan ba a magance matsalar ba, alummomi ka iya ɗaukar matakin kare kai wanda zai iya kai wa ga ƙazancewar rikicin da kuma kawo cikas ga dimokraɗiyyar ƙasar da zaman lafiyar yankin. "Muna kuma yi kira ga gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai da dama ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci domin ƙara duba girman lamarin, kuma ta aika jam'ian tsaro masu...
Gyaran da nawa Najeriya yasa a yanzu ana ganin Kima da darajarmu a Idon Duniya>>Inji Shugaba Tinubu

Gyaran da nawa Najeriya yasa a yanzu ana ganin Kima da darajarmu a Idon Duniya>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce muhimman tsare-tsaren gwamnatinsa sun soma samar da sakamakon da ake buƙata, inda ya ce tattalin arziƙin ƙasar ya daidaita har ya soma janyo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen duniya. Tinubu ya faɗi hakan ne a fadar sa da ke Abuja, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, a lokacin da ya karbi baƙuncin Oba Ghandi Afolabi Oladunni Olaoye, Orumogege III na Ogbomoso da tawagarsa. A cewar shugaban, halin ko-in-kula da rashawa da fasa kauri da yaudara ne su ka hana Najeriya samun kuɗaɗen shiga da za a yi amfani da shi wajen samar da ci gaba. ''Tattalin arziƙinmu ya fuskanci barazana, wajibi ne mu ɗauki matakai ƙwarara. Amma tare da adduo'in ku da haƙuri da juriyarku, ina farin cikin shaida muku cewa a yanzu tattalin arziƙi ya dai-daita'...
Jami’an tsaro na gani wasu abubuwan ke faruwa amma sai suce wai ba zasu dauki mataki ba saboda suna jiran Umarni>>Inji Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare

Jami’an tsaro na gani wasu abubuwan ke faruwa amma sai suce wai ba zasu dauki mataki ba saboda suna jiran Umarni>>Inji Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare

Duk Labarai
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya bayar da labarin cewa, a wasu lokutan jami'an tsaro na kallo wasu abubuwan ke faruwa amma sai su ce wai ba zasu iya daukar mataki ba suna jiran umarni daga sama. Ya bayyana hakane yayin hira da manema labarai. Dauda yace wasu lokutan har kuka yake. Yace abin takaici duk inda wani shugaban 'yan Bindiga yake a jiharsa ya sani kuma duk inda zasu yana sane amma babu abinda zai iya yi. https://twitter.com/AM_Saleeeem/status/1963549967643034005?s=19
Ina goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027, Kuma Kwankwaso ya mai mataimaki>>Inji Dan majalisa Abdulmumin Jibrin

Ina goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027, Kuma Kwankwaso ya mai mataimaki>>Inji Dan majalisa Abdulmumin Jibrin

Duk Labarai
Dan majalisar tarayya daga jihar Kano, Abdulmumin Jibrin ya bayyana cewa, Yana goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce a shekarar 2027. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV. Yace dalilinsa shine yana son kamar yanda Arewa ta yi shekaru 8 akan mulki, itama kudu ta kammala shekaru 8. Yace yana mamakin dan Arewa ya rika cewa an cuci Arewa a tsarin karba-karba na mulki a Najeriya. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1963321987444424770?t=xvm4haloRuAuSdXvW_n7uQ&s=19
Kalli Bidiyo: Budurwa me wanke-wanke ta dauki hankula sosai inda da yawa ke cewa aikin bai dace da ita ba

Kalli Bidiyo: Budurwa me wanke-wanke ta dauki hankula sosai inda da yawa ke cewa aikin bai dace da ita ba

Duk Labarai
Wannan Budurwar me wanke wake a wajan sayar da abinci ta dauki hankula sosai inda da yawa ke cewa aikin bai dace da ita ba. Bidiyonta na ta yawo a kafafen sada zumunta inda da yawa ke yabawa ds kyawunta. https://twitter.com/The__Vyrus/status/1963238904951091348?t=RXudu-DZBYlJB9qB2Hl_vQ&s=19 Wani dai yace yana son a nemo mai ita.
Duk budurwar da Saurayi ya aika mata da kudin mota da niyyar cewa ta je ta sameshi amma ta ki zuwa zata iya fuskantar hukunci, Hukumar ‘yansandan Najeriya ta gargadi ‘yan mata

Duk budurwar da Saurayi ya aika mata da kudin mota da niyyar cewa ta je ta sameshi amma ta ki zuwa zata iya fuskantar hukunci, Hukumar ‘yansandan Najeriya ta gargadi ‘yan mata

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya reshen jihar Rivers sun gargadi 'yan mata dake karbar kudin mota a hannub samari da niyyar cewa zasu je a hadu amma su ki zuwa. Hukumar tace hakan laifi ne na zamba cikin aminci da kuma samun kudi ta hanyar karya, hukumar tace idan saurayi ya shigar da kara, za'a iya hukunta budurwar. Kakakin 'yansandan jihar, Grace Iringe-Koko ce ta bayyana hakan a shafinta na X inda ta jawo hankalin mutane su daina neman kudi ta hanyar da bata dace ba.
Bidiyo Gwanin ban Sha’awa: Kalli Yanda kasar Yèmèn ta yi bikin murnar Haihuwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da ya kayar sosai ake ta yabawa

Bidiyo Gwanin ban Sha’awa: Kalli Yanda kasar Yèmèn ta yi bikin murnar Haihuwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da ya kayar sosai ake ta yabawa

Duk Labarai
Kasar Yemen ta yi bikin murnar haihuwar fiyayyen Halitta, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ta hanyar mamaye babban birninta da kalar Shudi. An kuma rika harba wuta me kara da ake kira da fire works. Lamarin ya kayar sosai inda mutane ke ta yabawa. https://twitter.com/GlobeEyeNews/status/1963326598398317012?t=z6l4eNEV90CI7x2w-cJGTA&s=19 Allahumma Salli Ala Mohammad wa ala ali Muhammad, kama Sallaita Ala Ibrahim wa ala ali Ibrahim fil alamin Innaka hamidum majid Allahumma Barik ala Muhammad wa'ala Ali Muhammad kama barakta Ala Ibrahim wa ala ali Ibrahim innaka hamidummajid