Tuesday, December 16
Shadow
Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutun Maulidi

Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutun Maulidi

Duk Labarai
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana Juma'a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutu domin bikin Maulidi na tunawa da ranar haihuwar annabi Muhammad (S.A.W). Gwamnatin ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ta fitar ranar Laraba, wadda ta samu sa hannun babbar sakatariya a ma'ikatar, Magdalene Ajani. Miliyoyin al'ummar Musulmi ne ke bukukuwan Maulidi a Najeriya da kuma faɗin duniya a duk irin wannan lokaci, kowace shekara. Sanarwar da gwamnatin Najeriyar ta fitar ta buƙaci al'ummar ƙasar su yi amfani da lokacin wajen yin addu'o'in samun zaman lafiya a ƙasar, wadda ke fama da matsaloli na tsaro.
APC ce silar matsalar tsaro a Najeriya ita ta kawo matsalar dan ta kawar da Jonathan daga kan mulki>>Inji Datti Baba Ahmad

APC ce silar matsalar tsaro a Najeriya ita ta kawo matsalar dan ta kawar da Jonathan daga kan mulki>>Inji Datti Baba Ahmad

Duk Labarai
Datti Baba Ahmad wanda dan takarar mataimakin shugaban kasa ne a jam'iyyar Labour party a shekarar 2023 ya bayyana cewa, jam'iyyar APC ce ta kawo matsalar tsaro da ake fama da ita a Najeriya. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace APC ce ta kawo matsalar tsaro a kokarin kawar da gwamnatin Tsohon shugaban kasa Jonathan. Yace wannan martanine maganar da El-Rufai yayi kan matsalar tsaro.
Wata Sabuwa: Gwamnatin tarayya ta cire Tallafin CNG wanda a baya ta kawo tace shine zai maye man fetur ta fara bayar da tallafi a kanshi, Kuma har farashin ya tashi sosai

Wata Sabuwa: Gwamnatin tarayya ta cire Tallafin CNG wanda a baya ta kawo tace shine zai maye man fetur ta fara bayar da tallafi a kanshi, Kuma har farashin ya tashi sosai

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa farashin CNG wanda Gwamnatin Najeriyar ta kawo bayan cire tallafin man fetur tace shine zai maye man fetur ta kuma bayar da tallafi akansa farashinsa yayi sauki sosai a yanzu ta cire masa tallafi kuma har farashinsa ya nunka. Rahoton da muke samu daga Punchng ya tabbatar mana da cewa, farashin na CNG ya tashi ya kai Naira 450, ga manyan motoci inda kananan motoci kuma ke sha akan farashin 380. Shugaban shirin na CNG, Michael Oluwagbemi yaki daukar waya dan yin bayanin dalilin cire tallafin. Saidai wani na kusa dashi da bai so a kira sunansa ya tabbatarwa da Punchng chire tallafin inda yace yanzu tashoshin CNG din na sayar da shi a farashi mabanbanta amma ya danganta da kalar motar da mutum ya je sayen CNG din da ita.
Ashe matsalar ba ta Rashin Ilimi bace: Wallahi Nasan Yaran dan damisa guda 4 duk mahaddata Qur’anine>>Inji Rabeeat

Ashe matsalar ba ta Rashin Ilimi bace: Wallahi Nasan Yaran dan damisa guda 4 duk mahaddata Qur’anine>>Inji Rabeeat

Duk Labarai
Bayan rasuwar kasurgumin dan daba dake kaduna, Habu Dan Damusa, an rika samun mutane wasu na Allah wadai wasu kuma na jinjinawa gareshi. Wata me suna Rabeeat data bayyana cewa ta sanshi tace matsalar ba ta rashin Ilimi bace Tace yaransa guda 4 duk mahaddata Qur'anine inda tace PA dinsa ma mahaddacin Qur'anine. Tace Addu'a ce kawai mafita inda tace me unguwarsu da ya rika tsine musu shima yaransa duk sun shiga daba. Tace dan haka ida mutum ya musu Addu'a, kamar yawa 'ya'yansa ne.
Kalli Bidiyon: Sheikh Bin Usman ya mayarwa da Sheikh Maqari martani inda yace du wanda yace wanda baya Maulidi ba musulmi bane to yace sahabbai ba musulmai bane saboda basu yi Maulidi ba

Kalli Bidiyon: Sheikh Bin Usman ya mayarwa da Sheikh Maqari martani inda yace du wanda yace wanda baya Maulidi ba musulmi bane to yace sahabbai ba musulmai bane saboda basu yi Maulidi ba

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Bin Usman ya mayarwa da Sheikh Maqari martani kan ikirarin Sheikh Maqari na cewa, duk wanda ba ya maulidi ba musulmi bane. Sheikh bin Usman yace duk wanda yace wanda baya Maulidi ba musulmi bane to yace sahabbai ba musulmai bane dan basu yi maulidi ba. https://www.tiktok.com/@_sadiq_07/video/7544050335359307026?_t=ZS-8zP3p6xOleb&_r=1
Kotu ta soke dokar aikin Soja a Najeriya da ta ce dole sai soja yayi shekaru 15 yana aiki kamin a yadda yayi ritaya, Kotun tace soja na da ikon ajiye aiki a duk sanda yake so

Kotu ta soke dokar aikin Soja a Najeriya da ta ce dole sai soja yayi shekaru 15 yana aiki kamin a yadda yayi ritaya, Kotun tace soja na da ikon ajiye aiki a duk sanda yake so

Duk Labarai
Kotun Ma'aikata dake da zama a Abuja National Industrial Court ta soke dokar aikin soja da tace sai soja ya shafe shekaru 15 yana aiki kamin a yadda yayi ritaya. Kotun tace wannan doka ta sabawa kundin tsarin mulki dannan ta take hakkin sojojin wanda kundin tsarin mulki ya basu sannan ta bayyana dokar da cewa kamar bautar da sojojin ake. Dan haka tace ta soke wannan doka kuma a ko wane lokaci sojan Najeriya zai iya yin ritaya ya ajiya aiki. Mai shari'a, Justice Emmanuel D. Subilim ne ya yi wannan hukunci bayan da sojan sama, Flight Lieutenant J. A. Akerele.ya shigar da kara saboda yana son ya ajiye aiki amma an hanashi. Sojan yace an ki yi mai karin girma sannan ana ta wahalar dashi a gidan sojan inda wanda suka fara aiki tare an musu karin girma amma shi ba'a mai ba. Yace d...
Wata Sabuwa: Hon. Magaji Yarima Madachi Daga Jihar Bauchi ya tura 100k a asusun Uwar gidan Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu domin taya ta murna cika shekara 65 a duniya.

Wata Sabuwa: Hon. Magaji Yarima Madachi Daga Jihar Bauchi ya tura 100k a asusun Uwar gidan Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu domin taya ta murna cika shekara 65 a duniya.

Duk Labarai
Hon. Magaji Yarima Madachi Daga Jihar Bauchi ya tura 100k a asusun Uwar gidan Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu domin taya ta murna cika shekara 65 a duniya. Hon. Magaji Yarima Madachi (Dan Sararin Madachi) ya shiga jerin dubban masoya kuma magoya bayan Sen Oluremi Tinubu ta hanyar bada tasa gudummawar domin karasa aikin National Library kamar yadda ta bukata. Shi dai wannan matashi ya kasance dan jam'iyyar APC kuma mai rajin tsayawa matasa domin a temakesu. Muna Allah san Barka da wannan yunkuri nasa. Daga Ahmad Khamisu Madachi.
Sai na rage wa Tinubu ƙuri’a miliyan guda a 2027 – Kabiru Marafa

Sai na rage wa Tinubu ƙuri’a miliyan guda a 2027 – Kabiru Marafa

Duk Labarai
Tsohon Ɗan Majalisar Dattawan Najeriya mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya, Sanata Kabiru Marafa ya sha alwashin rage wa Tinubu ƙuri'u masu yawa a zaɓen 2027. Marafa, wanda a baya-bayan nan ya sanar wa BBC ficewarsa daga jam'iyyar APC, bayan ya zargi Tinubu da ''watsar da shi bayan cin zaɓe'' ya ce sai ya kawo wa shugaban ƙasar cikas a zɓen 2027 da ke tafe. Yayin wata hira da hgidan talbijin na Channels, Sanata Marafa ya ce sai ya janyo wa Tinubu asarar kimamin ƙuria' miliyan guda. Tsohon ɗan majalisar - wanda ya kasance babban daraktan yaƙin neman zaɓen Tinubu a Zamfara a 2027 - ya ce zai nuna wa shugaban ƙasar matsayinsa a siyasar jihar Zamfara.
Ban yi kuskure ba wajen zaɓen Kashim a matsayin mataimaki – Tinubu

Ban yi kuskure ba wajen zaɓen Kashim a matsayin mataimaki – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba da jajircewar mataimakinsa, Kashim Shettima, wanda ya bayyana da mutum mai amana da gaskiya da yake jin daɗin aiki da shi. A wata sanarwa da ya fitar kan taya mataimakin nasa murnar cika 59 a duniya, Tinubu ya ce, "tun da na sanka har zuwa yanzu, ba ka nuna gajiyawa wajen aiki tuƙuru domin sake gina ƙasarmu. A dukkan muƙaman da ka riƙe a baya, ka nuna jajircewa wajen aiwatar da abubuwan da suka dace duk runtsi duk wahala." Tinubu ya ce yana godiya bisa irin goyon bayan da yake samu daga Shettima, "lokacin da na zaɓe ka a matsayin mataimakina, na san ban yi zaɓen tumun-dare ba, na san na ɗauko nagartacce wanda Najeriya za ta yi alfahari da shi. Kullum a aikinka na mataimaki, kana ƙoƙari wajen kawo shawarwari da tsara sababbin abubuwa da za su taim...