Thursday, May 22
Shadow

Gwamnoni sun kai ziyarar jaje zuwa Maiduguri

Duk Labarai
Gwamnonin wasu jihohin Najeriya sun ziyarci birnin Maiduguri domin jajanta wa gwamnati da al'ummar jihar bisa iftila'in ambaliya da ya auka wa birnin. Gwamnonin da suka ziyarci Maidugurin sun haɗa da na Legas Babajide Sanwo Olu da na Ondo, Lucky Aiyedatiwa da na Adamawa, Umar Fintiri da kuma na Kwara, Abdulrahman AbdulRazaq. Gwmanan Legas - wanda ya bayyana ambaliyar a matsayin mummuna - ya ce gwamnonin sun jajanta wa iyalan mutanen da lamarin ya shafa, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X. ''A matsayinmu na al'umma ɗaya yana da muhimmanci mu haɗa kai don samar da agaji da taimaka wa aikin ceto, tare da tabbatar da cewa waɗanda lamarin ya shafa sun samu tallafin da suke buƙata'', in ji Gwamnan Sanwo Olu.
Gwamnan Zamfara ya ɗauki nauyin karatun zaƙaƙuran ɗaliban jihar

Gwamnan Zamfara ya ɗauki nauyin karatun zaƙaƙuran ɗaliban jihar

Duk Labarai
Gwamnan jihar Zamfara a arewacin Najeriya ya ba wa wasu zaƙaƙuran dalibai 30 tallafin karatu domin su yi karatu a sakandiren gwamnatin tarayya ta Federal Government Academy da ke Suleja ta jihar Neja. Gwamna Dauda Lawal ya bayyana hakan ne a yau Alhamis lokacin da yake ganawa da ɗaliban da kuma jagorancin Cibiyar Muhammad Kabir Danbaba Centre for Women and Youth Development Center a fadar gwamnatin jihar da ke Gusau. Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya ce cibiyar tana taka muhimmiyar rawa wajen nasarar da jihar ta Zamfara ke samu a ɓangaren ilimi. Sanarwar ta ƙara da cewa yawancin ɗaliban da suka fi samun nasara na makarantun gwamnati ne. "Wannan nasarar da kuka samu ta nuna cewa gwamnatinmu na ƙoƙari wajen inganta ilimi," a cewar Gwamna Dauda Lawal.
Shugaba Tinubu ya gana da Sarki Charles na Ingila

Shugaba Tinubu ya gana da Sarki Charles na Ingila

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana Sarki Charles na Ingila a fadarsa ta Buckingham da ke birnin Landan. Mai taimaka wa shugaban ƙasa kan yaɗa labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga, shi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis. Sanarwar ta bayyana ganawar a matsayin ta sirri, wadda ta ƙara nuna alaƙar da ke tsakanin Najeriya da Birtaniya. "Shugabannin sun tattauna batutuwan da suka shafi ƙasashensu, musamman matsalar sauyin yanayi," kamar yadda sanarwar ta bayyana. Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu da Sarki Charles sun tattauna hanyoyin da za su iya yin haɗaka musamman a daidai lokacin da ake shirin taron COP 29 da ke tafe a ƙasar Azerbaijan da kuma taron ƙasashe rainon Ingila wato CHOGM da za a yi a Samoa. Ya ce: "Tinubu ya ƙara nanata ƙudurin Najeriya na...
Tinubu ya bai wa jihohi naira biliyan 108bn kan ambaliya da zaizayar ƙasa – Shettima

Tinubu ya bai wa jihohi naira biliyan 108bn kan ambaliya da zaizayar ƙasa – Shettima

Duk Labarai
Tinubu ya bai wa jihohi naira biliyan 108bn kan ambaliya da zaizayar ƙasa - Shettima. Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da kuɗi Naira biliyan 108 ga jihohi 36 na ƙasar domin yaƙi da ambaliya da sauran nau'ukan bala'o'i. Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa a ranar Laraba. Da yake bayyani a lokacin da ya karɓi baƙuncin Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya, Abbas Tajudden, ya bayyana ambaliyar ta Borno a matsayin "bala'i ga ƙasar baki ɗaya." "Shugaba ƙasar ya nuna niyyarsa ta haɗa hannu da jihohi domin magance irin waɗannan matsalolin," inji Shettima. "Ba a daɗe ba ya amince a ba kowace jiha Naira biliyan uku domin magance irin waɗannan matsalolin," kamar yadda shafin talabijin na Ch...
IMF ya nemi Tinubu ya tausaya wa talakawan Najeriya

IMF ya nemi Tinubu ya tausaya wa talakawan Najeriya

Duk Labarai
A daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara a kan ƙarin farashin man fetur, Asusun Lamuni na Duniya, IMF, ya buƙaci gwamnatin Najeriya da ta ba ɓangaren rage wa talakawan ƙasar raɗaɗi muhimmanci. Da yake jawabi a tattaunawarsa da gidan talabijin na Arise TV a jiya, babban wakilin IMF a Najeriya, Dokta Christian Ebeke ya ce har yanzu ba a kai farashin man fetur ɗin asalin farashinsa na kasuwa ba, wanda hakan ke nuna cewa za a ƙara farashin a nan gaba kamar yadda jaridar Vanguard ta kalato. Idan ba a manta ba, shi ma kamfanin NNPCL na Najeriya ya bayyana irin wannan matsayar a baya. Babban jami'in na IMF ya bayyana damuwarsa a kan irin wahalar da ƴan Najeriya suke ciki a sanadiyar wasu matakai da gwamnatin ƙasar ta ɗauka. A cewar Ebeke, "Ina tunanin ƙarin farashin man ya zo ne a ...
WATA SABUWA: Saura kaɗan mu kama Bello Turji – Janar Chris Musa

WATA SABUWA: Saura kaɗan mu kama Bello Turji – Janar Chris Musa

Duk Labarai
Babban hafsan tasro na Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ci alwashin kama ƙásurgųmi kuma jagorán 'yaɲ fáshíɲ daji Bello Turji "nan ba da jimawa ba". BBC ta rawaito Musa yana magana yayin wani taron manema labarai ranar Talata a Abuja, janar ɗin ya ce: "Saura kaɗan mu kama Turji." Game da wa'adin biyan kuɗin haraji da aka ce Turji ya bai wa mazauna yankunan jihar Zamfara, Janar Musa ya ce sojoji na aiki da sauran hukumomin tsaro domin kare mazauna yankunan. "Game da Turji, mutum ne kawai da ya sauka daga kan layi kuma yake tunanin ya isa, amma ina tabbatar muku za mu kamo shi kuma cikin ƙanƙanin lokaci," in ji shi. Shugaban sojojin ya kuma nemi mazauna yankunan da su bai wa sojoji haɗin kai. "Kada ku taimaka musu, kada ku ba su wasu bayanai game da samamen da muke kaiwa sa...
Hotuna: Matashi ya kashe kansa bayan da Talauci ya masa yawa bai iya ciyar da iyalansa, matarsa ta koma yin lalata da abokansa suna bata kudi

Hotuna: Matashi ya kashe kansa bayan da Talauci ya masa yawa bai iya ciyar da iyalansa, matarsa ta koma yin lalata da abokansa suna bata kudi

Duk Labarai
Wannan matashin na zaunene a Masaka, Angwa Jaba, dake karamar hukumar Karu. Ya kashe kansa ranar 9 ga watan Satumba. Talauci ne ya masa yawa baya iya ciyar da iyalansa, kuma ya gano matarsa tana yin lalata da abokansa dan ta samu kudi. Koda ya tuhumeta akan hakan tace masa tana neman hanyat da zata tallafa musu samun abinci ne. Suna da yara 3, magidancin ya ji cewa abin ya masa yawa dan hakane ya dauki rayuwarsa.
‘Yan Banga a jihar Naija sun yi nasarar kashe ‘Yan Boko Haram da dama

‘Yan Banga a jihar Naija sun yi nasarar kashe ‘Yan Boko Haram da dama

Duk Labarai
Zaratan 'yan Banga a garin Alawan da Bassa dake jihar Naija sun yi nasarar kashe 'yan Boko Haram da dama. Rahoton da hutudole ya samu daga wata majiya dake yankin ya bayyana cewa lamarin ya faru sa sanyin safiyar ranar Laraba. 'Yan bangan sun kashe da dama daga cikin maharan inda suka kama wasu da ransu. Hutudole ya ga gawarwakin 'yan Boko Haram din amma saboda muninsu yasa ba zamu iya wallafasu anan ba. Maharan dai su 20 ne inda auka yi nasarar kashe mutane 2 da harbin mutum daya hakanan a cikin 'yan bangar ma, an kasheutane biyu.

Gyaran fuska da ayaba

Gyaran Fuska
Ayaba na daya daga cikin kayan itatuwan da ake ci amma amfaninta ba ga ci a ciki a koshi bane kawai, tana kuma da amfani wajan gyaran jiki, musamman fuska. Daya daga cikin Amfanin Ayaba a fuska shine, musamman wadanda suka fara manyanta, fuska ta fara tattarewa, Ayaba na taimakawa matuka wajan gyara tattarar fuska wandda ke zuwa sanadin tsufa. Hakanan tana yakar abubuwan da ake kira da Free Radicals wanda sune ke saurin kawo tsufa ga fata. Ayaba tana taimakawa matuka wajan boye kurajen fuska, amfani da ita a fuska yana kwantar da kumburin kuragen fuska ya zamana kamar babusu. Hakanan Ayaba tana boye tabon fuska da shacin rana da yakewa fuska. Hakanan tana baiwa fatar jiki kariya daga duhun zafin rana, ma'ana idan aka shafata aka shiga rana, zafin ranar ba zai cutar ba. Ha...

Gyaran fuska da tafarnuwa

Gyaran Fuska
Tafarnuwa na da matukar amfani musamman a wajan gyaran fuska. Ana amfani da tafarwa dan kawar da kurajen fuska da duk wani dattin fuska,hakanan amfani da ita a fuska yana maganin abubuwan dake kawo saurin tsufa. Hakanan Tafarnuwa na disashe girman tabo a fuska. Masana kiwon Lafiya sun bayyana cewa, goga Tafarnuwa a kan kurajen fuska yana taimakawa sosai wajan magance kurajen. Saidai a bi a hankali, Tafarnuwa na sawa a ji zafi ko kaikayi a yayin da aka sa ta a fuska. Ba kowane tafarnuwa za iyawa aiki ba, saboda wasu idan suka shafata a fuskarsu, zata iya yi musu illa sosai wajan sa kai kai ko zafi. Dan haka a shawarce, a dan shafata a wani bangare kadan na fuska a ga yanda zata yi, idan ba'a ji ko mai ba, sai a shafa a sauran duka fuskar. Hakanan yana da kyau a hada taf...