Tauraruwar Kannywood, Momee Gombe kenan a wannan Bidiyon inda ta nuna katafaren gidan da ta saya a Kano.
Bidiyon gidan ya karade kafafen sada zumunta inda akai ta tayata murna.
https://www.tiktok.com/@kannywoodtv1/video/7544324471163850006?_t=ZS-8zMO9gwg9Eu&_r=1
Tsohon gwanan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu har kudi take biyan 'yan Bindiga duk wata.
Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace bayan haka har kayan abinci gwamnatin ke aikawa 'yan Bindigar.
El-Rufai ya kara da cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zaben 2027 ba na uku zai zo.
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayar da martani ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kan sukar da ya masa a gidan talabijin na Channels TV.
Shugaban ya mayar da martanin ne ta bakin me magana da yawunsa, Bayo Onanuga ta kafar X.
Ya rubuta cewa a shekarun baya, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yace shekaru 4 sun yiwa shugaban kasa kada ya gyara Najeriya ko ya kawo ci gaba amma yanzu yana sukarsa.
Yace amma duk da haka ya kawo abubuwan ci gaba Najeriya sosai.
Misali an samu habakar arziki sosai ta bangaren kasuwar hannun jari inda aka samu karuwar dukiya data kai naira Tiriliyan 26.
Tauraruwar fina-finan Hausa, Firdausi Yahya ta bayyana cewa, tana son aure.
Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita inda tace idan ta samu me sonta itama tana sonshi, zata yi aure.
Da aka tambayeta wane kalar miji take so?
Sai ta kayar da baki tace zabin Allah take so.
https://www.tiktok.com/@abdullahee40/video/7544879991218097415?_t=ZS-8zMHgM750Mq&_r=1
Wannan malamin ya fito ya sassauta lafazi akan wa'azi me kaushi da yayi a baya akan rasuwar dan daba, Habu Dan Damisa na Kaduna.
Malam a yanzu yace, a dauna munana zato akan dan Damisa inda yace lamarinsa na ga Allah, in yaso ya azabtar dashi in yaso ya yafe masa.
https://www.tiktok.com/@ib_yusuf_muhd_sambo/video/7544714115546221842?_t=ZS-8zMBsjILGvh&_r=1
Saidai da yawa sun ce malamin tsoro yaji kada yaran dan Damisa su illatashi ko kumama aikashi kiyama.
A baya dai malam yayi Allah wadai da irin rayuwar dan Damisa inda ya kushe harkar daba duk da dai wa'azi ne yayi.
https://www.tiktok.com/@ib_yusuf_muhd_sambo/video/7543712129984056584?_t=ZS-8zMGbsPoGDR&_r=1
Akwai wani matashi da ya fito yayi zagezage akan malamai, sannan ko a kasan Bidiyon malam an ga yanda a...
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, babu wanda yasa Gwamnatin Tinubu kamarshi.
Yace dan haka shedaniyar Gwamnati ce da babu abinda ya kawota dai satar dukiyar talakawa.
El-Rufai ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV.
Gwamna Uba Sani Ba Abokina Ba Ne, Yarona Ne A Siyasa, Cewar Elrufa'i.
Wannan kalamai na El-Rufai na zuwane bayan da 'yan daba suka tarwatsa taron jam'iyyar su ta ADC a Jihar.
El-Rufai dai ya zargi Uba sani da cewa shine ya tura musu 'yan daba.
An ga yanda 'yan daba ke zuwa suna gaisuwar Habu Dan Damisa a Kaduna suna faduwa kasa suna kirari da zagezage.
Hakan yasa wasu fadin cewa, da alama har yanzu tsugune bata kare ba.
https://www.tiktok.com/@kabiruabdulsalamy6/video/7544733132801527058?_t=ZS-8zLeGCoTTeb&_r=1
Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Yahya Kenan a wannan Bidiyon nata da aka ganta a wajan wani biki.
Bidiyon dai ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa shigar tata bata dace ba
https://www.tiktok.com/@mistinbestiebackup/video/7544876237164924168?_t=ZS-8zLd5QUaC6j&_r=1
Tsohon gwamnan jihar Kaduna malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa yayi iya lissafinsa bai ga ta yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sake con zabe ba a 2027.
Ya bayyana hakane hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace Tinubu na 3 zaizo a zaben.
Yace amma akwai yiyuwar za'a yi saben zagaye na biyu dan da wuya a samu wanda yayi nasara a zagayen farko.