Tuesday, March 3
Shadow
Wata Sabuwa: El-Rufai yawa Gwamnatin Tinubu tonon Silili inda ya fadi yanda suke biyan ‘yan Bìndìgà Albashi duk wata

Wata Sabuwa: El-Rufai yawa Gwamnatin Tinubu tonon Silili inda ya fadi yanda suke biyan ‘yan Bìndìgà Albashi duk wata

Duk Labarai
Tsohon gwanan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu har kudi take biyan 'yan Bindiga duk wata. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace bayan haka har kayan abinci gwamnatin ke aikawa 'yan Bindigar. El-Rufai ya kara da cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zaben 2027 ba na uku zai zo.
Kai ka taba cewa shekaru 4 sun yi kadan shugaba ya kawo canji a Najeriya amma gashi yanzu kana sukata>>Shugaba Tinubu ga El-Rufai

Kai ka taba cewa shekaru 4 sun yi kadan shugaba ya kawo canji a Najeriya amma gashi yanzu kana sukata>>Shugaba Tinubu ga El-Rufai

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayar da martani ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kan sukar da ya masa a gidan talabijin na Channels TV. Shugaban ya mayar da martanin ne ta bakin me magana da yawunsa, Bayo Onanuga ta kafar X. Ya rubuta cewa a shekarun baya, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yace shekaru 4 sun yiwa shugaban kasa kada ya gyara Najeriya ko ya kawo ci gaba amma yanzu yana sukarsa. Yace amma duk da haka ya kawo abubuwan ci gaba Najeriya sosai. Misali an samu habakar arziki sosai ta bangaren kasuwar hannun jari inda aka samu karuwar dukiya data kai naira Tiriliyan 26.
Kalli Bidiyo:Ina son aure, idan na samu wanda ke sona ima ina sonshi, zan yi Aure>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Firdausi Yahya

Kalli Bidiyo:Ina son aure, idan na samu wanda ke sona ima ina sonshi, zan yi Aure>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Firdausi Yahya

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Firdausi Yahya ta bayyana cewa, tana son aure. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita inda tace idan ta samu me sonta itama tana sonshi, zata yi aure. Da aka tambayeta wane kalar miji take so? Sai ta kayar da baki tace zabin Allah take so. https://www.tiktok.com/@abdullahee40/video/7544879991218097415?_t=ZS-8zMHgM750Mq&_r=1
Allah Sarki: Kalli bidiyon Yanda wannan malamin ya sassauta lafazi akan Rasuwar Habu Dan Damisa, Yace Lamarinshi na gurin Allah a daina munana masa zato, bayan da a baya yayi wa’azi me kaushi sosai akan Dan Damusa amma yaran Dan Damusa suka gargadeshi

Allah Sarki: Kalli bidiyon Yanda wannan malamin ya sassauta lafazi akan Rasuwar Habu Dan Damisa, Yace Lamarinshi na gurin Allah a daina munana masa zato, bayan da a baya yayi wa’azi me kaushi sosai akan Dan Damusa amma yaran Dan Damusa suka gargadeshi

Duk Labarai
Wannan malamin ya fito ya sassauta lafazi akan wa'azi me kaushi da yayi a baya akan rasuwar dan daba, Habu Dan Damisa na Kaduna. Malam a yanzu yace, a dauna munana zato akan dan Damisa inda yace lamarinsa na ga Allah, in yaso ya azabtar dashi in yaso ya yafe masa. https://www.tiktok.com/@ib_yusuf_muhd_sambo/video/7544714115546221842?_t=ZS-8zMBsjILGvh&_r=1 Saidai da yawa sun ce malamin tsoro yaji kada yaran dan Damisa su illatashi ko kumama aikashi kiyama. A baya dai malam yayi Allah wadai da irin rayuwar dan Damisa inda ya kushe harkar daba duk da dai wa'azi ne yayi. https://www.tiktok.com/@ib_yusuf_muhd_sambo/video/7543712129984056584?_t=ZS-8zMGbsPoGDR&_r=1 Akwai wani matashi da ya fito yayi zagezage akan malamai, sannan ko a kasan Bidiyon malam an ga yanda a...

Na yi iya lissafin da zan yi na gano cewa, Tinubu ba zai ci zaben 2027 ba, na kudu zai zo>>Inji El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa yayi iya lissafinsa bai ga ta yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sake con zabe ba a 2027. Ya bayyana hakane hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace Tinubu na 3 zaizo a zaben. Yace amma akwai yiyuwar za'a yi saben zagaye na biyu dan da wuya a samu wanda yayi nasara a zagayen farko.