Wednesday, March 4
Shadow
Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Duk Labarai
Mata a birnin Legas sun yi barazanar yin zanga-zangar tsirara dan tursasa daina rushe musu gidaje. Matan daga yankin Ilaje sun yi zanga-zangar lumana zuwa majalisar dokokin jihar ta Legas inda suka nemi taimakon gwamnan jihar, Babajide Sonwo Olu da kakakin majalisar Dokokin jihar,Mudashiru Obasa su saka baki a daina rushe musu gidaje. Sun zargi sarakunan gargajiyarsu da yi musu kwacen gidaje. Daya daga cikin matan wadda dattijuwa ce, ta fito inda take barazanar cewa, zasu yi zanga-zanga tsirara idan ba a daina rushe musu gidaje ba. Shima shugaban mazauna yankin na Ilaje, Rafael Irowainu ya bayyana cewa wasu sarakuna na amfani da sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suna rushe gidaje dan su yi gine-gine. Ya kara da cewa, amma basu yadda shugaba ne ya aika mutanen ba.
Sai an kawo mana dauki, Lamuran tsaro sun ta’azzara>>Inji Gwamnan riko na jihar Katsina, wanda Gwamna Radda ya barwa jihar a hannunsa

Sai an kawo mana dauki, Lamuran tsaro sun ta’azzara>>Inji Gwamnan riko na jihar Katsina, wanda Gwamna Radda ya barwa jihar a hannunsa

Duk Labarai
Gwamnan riko na jihar Katsina wanda gwamna Dikko Radda ya barwa jihar a hannunsa Malam Faruk Lawal-Jobe ya yi kira ga gwamnatin tarayya data kawo musu dauki a jihar game da tabarbarewar lamuran tsaro. Wannan kira nasa na zuwane bayan harin da 'yan Bindiga suka kai unguwar Muntau dake garin Malunfashi a jihar Katsina suka kashe mutane akalla 13 dake sallar Asuba. Hakanan maharan sun rika harbin kan mai uwa da wabi inda kuma suka sace mutane 60, kamar yanda kafar Rariya ta tuwaito. Hakan na zuwane a yayin da Gwamna Dikko Radda ke kasashen Turawa nema Lafiya amma an hangoshi a wasu hotuna yana daukar hoton garin da yaje. Gwamnan rikon, Malam Faruk Lawal-Jobe ya nemi gwamnatin tarayya data kawowa jihar dauki lura da yanda lamuran tsaro suka tabarbare tare da neman Shugaban kasa ya ...
Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa da ake shirin yi. Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida ne ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai. Yace karin harajin kaso 5 akan kamfanonin sadarwar yana kunshene a cikin sabon kudirin dokar da majalisa ta amince dashi. Yace yana wajan aka kawowa shugaba Tinubu maganar karin amma yace ba zai kara saka 'yan Najeriya a cikin matsala ba. Yace a baya an dakatar da karinne amma yanzu an cireshi gaba daya.
Ina son shiga Aljannah>>Inji Shugaban kasar Amurka, Donald Trump

Ina son shiga Aljannah>>Inji Shugaban kasar Amurka, Donald Trump

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana son shiga Aljannah. Ya bayyana cewa dalili ma kenan da yake ta kokarin ganin ya kawo karshen yakin kasashen Russia da Ukraine. A baya Shugaba Trump ya gana da shugaban kasar Russia, Vladimir Putin sannan ya gana da shugaban kasar Ukràìnè sa shuwagabannin kasashen Turai. A nan gaba yace zai hada Putin da Zelenskyy su yi zaman sulhu. Tun kamin ya zama shugaban kasa yayi Alkawarin cewa idan ya ci zabe, zai tabbatar ya kawo karshen yakin.
Hukumar Shirya fina-finai ta Najeriya ta yi martani yayin da ake rade-radin Ali Nuhu ya rigamu gidan gaskiya

Hukumar Shirya fina-finai ta Najeriya ta yi martani yayin da ake rade-radin Ali Nuhu ya rigamu gidan gaskiya

Duk Labarai
Hukumar shirya fina-finai ta kasa, NFC ta musanta Bidiyon dake yawo a kafafen sadarwa dake ikirarin cewa, shugabanta, Ali Nuhu ya mutu. Jaridar Leadership tace NFC ta gaya mata cewa wannan rashin kyautawa ne da kuma abin Allah wadai inda hukumar ta nemi gwamnati ta saka ido akan kafafen sadarwa da kula da gudanarwarsu. Daraktan yada labarai na hukumar, Brian Etuk ya bayyana cewa, Ali Nuhu na nan lafiyarsa qalau. Yace kuma suna nan suna shirin daukar matakin da ya dace kan lamarin.
Fadar shugaban ƙasa ta yaba da ƙwazon Ribadu a matsayin NSA a watanni 25 da fara aiki

Fadar shugaban ƙasa ta yaba da ƙwazon Ribadu a matsayin NSA a watanni 25 da fara aiki

Duk Labarai
Fadar shugaban ƙasa ta yaba da ƙwazon Ribadu a matsayin NSA a watanni 25 da fara aiki Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa watanni 25 da Malam Nuhu Ribadu ya kwashe a matsayin Mai baiwa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA) sun zama juyin juya hali a yaki da ta’addanci, ’yan fashi da makami da sauran barazanar tsaro. Mataimakin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan kafafen sada zumunta, Dada Olusegun, ya ce nadin Ribadu ya samar da sakamako a fili, ciki har da cafke manyan masu hannu a hare-haren ta’addanci, rage yawaitar hare-haren ’yan fashi a Arewa maso Yamma, ƙaruwar man fetur da ake samarwa ƙasa da miliyan ɗaya zuwa kusan miliyan 1.8 a kowace rana, da kuma rage rikicin ƙabilanci a wasu jihohi. Haka kuma, ya ce Ribadu ya taka muhimmiyar rawa wajen raunana kungiyar IPOB/ESN...