Monday, December 15
Shadow
Ya kamata ku fahimci cewa, babu dan siyasar da ‘yan Adawa zasu hada kai su taso suna son kayar dashi mulki irin yanda ake min kuma yayi shiru yaki magana>>Shugaba Tinubu

Ya kamata ku fahimci cewa, babu dan siyasar da ‘yan Adawa zasu hada kai su taso suna son kayar dashi mulki irin yanda ake min kuma yayi shiru yaki magana>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, babu dan siyasar da 'yan Adawa zasu hada kai su taso suna son kayar dashi mulki kamar yanda ake masa, amma yayi shiru yaki yin magana. Shugaban ya jawo hankalin 'yan Najeriya da cewa su daina baiwa 'yan siyasar dake son kayar dashi zabe a 2027 muhimmanci. Ya bayyana hakane a yayin ziyarar da ya kai jihar Nasarawa inda ya kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da gwamnatin jihar ta gudanar.
Ji bayani dalla-dalla yanda Ministan Abuja Nyesom Wike ya baiwa dansa filiye dubu arba’in a Abuja wanda kudinsau sun kai dala Biliyan $3.6, yace so yake ‘ya’yansa su zamana sun fi kowa yawan filaye a Abuja

Ji bayani dalla-dalla yanda Ministan Abuja Nyesom Wike ya baiwa dansa filiye dubu arba’in a Abuja wanda kudinsau sun kai dala Biliyan $3.6, yace so yake ‘ya’yansa su zamana sun fi kowa yawan filaye a Abuja

Duk Labarai
Ana zargin ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike da baiwa dansa wani babban fili a Abujan wanda darajarsa ta kai Dala Biliyan $3.6. Kafar Peoplesgazette ce ta ruwaito labarin inda ta bayyana wasu kafofin da suka tabbatar mata da faruwar hakan wanda aka ce sabawa dokane. Wike wanda tun watan Augusta na shekarar 2023 yake akan mukamin Ministan Abuja, ya baiwa dan nasa me suna Joaquin Wike filin da ya kai girman Hecta 2000, kamar yanda rahoton ya bayyanar. Rahoton yace Wike bai bi doka ba wajan baiwa dan nasa wannan makeken fili ba sannan kuma bai ma biya kudaden da ya kamata a biya ba. Sannan ya baiwa dan nasa Filayen ne a manyan unguwannin Abuja da suka hada da Maitama, Asokoro, Guzape, Bwari, da Gaduwa. Yawan filayen sun kai Dubu 40. Wani Hadimin Wiken yace s...
Yanzu na kammala canja komai a jikina na zama cikakkiyar mace>>Inji Dan Daudu, Idris Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky

Yanzu na kammala canja komai a jikina na zama cikakkiyar mace>>Inji Dan Daudu, Idris Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky

Duk Labarai
Shahararren dan Daudu, Idris Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky ya bayyana cewa, a yanzu ya kammala canja komai na jikinsa inda ya zama cikakkiyar mace. Bobrisky ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na sada zumunta. Yace yana son a yanzu a rika kiransa da sunan Afolashade Amope. Yace shima yanzu za'a iya yin jima'i dashi kamar yanda ake yi da kowace mace. Ya lokaci yayi da mutane zasu amince da hakan inda ya taya kansa murna. Kuma yacw yana Alfahari da kansa.
Cristiano Ronaldo ya sabunta Kwantirakinsa da Kungiyar Al Nasr, Ji damar da suka bashi ta ban mamaki

Cristiano Ronaldo ya sabunta Kwantirakinsa da Kungiyar Al Nasr, Ji damar da suka bashi ta ban mamaki

Duk Labarai
Tauraron dan kwallon Portugal, Cristiano Ronaldo ya sabunta kwantirakinsa da kungiyar Al Nasr ta kasar Saudiyya. Daga cikin damarmakin da aka bashi shine yana da bakin magana akan duk dan wasan da kungiyar zata siya. Ronaldo dan shekaru 40 ya amince da ci gaba da zama a kungiyar ta Al Nasr har zuwa shekarar 2027. Tun a shekarar 2023 ne dai Ronaldo ya je kungiyar ta Al Nasr.
‘Yan Kwaya sun karu a Najeriya>>Gwamnatin Tinubu ta koka

‘Yan Kwaya sun karu a Najeriya>>Gwamnatin Tinubu ta koka

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnatin tarayya ta koka da cewa, 'Yan kwaya sun karu a Najeriya. Hakan na zuwane yayin da ake tunawa da zagayowar ranar yaki da shan kwaya da safararta a Duniya. Gwamnatin ta yi kiran hada kai dan yakar wannan matsala. Babbar sakatariya a ma'aikatar lafiya ta tarayya, Daju Kachollom, cee ta bayyana hakan a ganawa da manema labarai. Tace matsalar ta'ammuli da miyagun kwayoyi ba matsalar mutum daya bace ko kuma masu sha kawai, matsala ce ta kowa da kowa dan haka hadin kai...
Karanta Jadawalin Gwamnonin Babban Bankin Najeriya CBN da aka taba yi da shekarun da suka yi suna rike da mukaman

Karanta Jadawalin Gwamnonin Babban Bankin Najeriya CBN da aka taba yi da shekarun da suka yi suna rike da mukaman

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} 1 Abdulkadir Ahmed — 11 years, 97 days 2 Godwin Emefiele — 9 years, 8 days 3 Clement Nyong Isong — 8 years, 40 days 4 Paul Agbai Ogwuma — 5 years, 241 days 5 Joseph Oladele Sanusi — 5 years, 2 days 6 Ola Vincent — 5 years, 1 day 7 Charles Soludo — 5 years, 1 day 8 Lamido Sanusi — 4 years, 263 days 9 Aliyu Mai-Bornu — 3 years, 333 days 10 Olayemi Cardoso — 1 year, 284 days 11 Adamu Ciroma — 1 year, 278 days
Darajar Naira na ci gaba da faduwa a kasuwar Canji

Darajar Naira na ci gaba da faduwa a kasuwar Canji

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Darajar Naira na ci gaba da faduwa a kasuwar Canji. Rahotannin yanda kasuwar ta kasance a ranar Laraba na cewa, an sayi dala akan Naira N1,549.26 wanda hakan ya nuna darajar Nairar ta fadi idan aka kwatanta da yanda aka sayi dalar akan Naira N1,549.04 a ranar Talata. Nairar ta rasa darajar Kwabo N0.22. Wannan farashin kasuwar Gwamnati ne. A kasuwar 'yan bayan fage kuwa Dalar an saye ta ne akan Naira N1,590 a ranar Laraba inda hakan ke nuna darajar Nairar ta dan tashi da Naira 5 idan aka kwatanta farashin da aka saye ta na Naira N1,595 a ranar Talata.
Kalli Bidiyo: Mijina bai iya soyayya ba, ko Kis bai taba min ba tunda muka yi aure, kullun kawai saidai ya zo yace in bude mai>>Matar aure ta kaiwa Fasto karar Mijinta

Kalli Bidiyo: Mijina bai iya soyayya ba, ko Kis bai taba min ba tunda muka yi aure, kullun kawai saidai ya zo yace in bude mai>>Matar aure ta kaiwa Fasto karar Mijinta

Duk Labarai
Wata matar aure ta dauki hankula bayan kai karar Mijinta wajan Fasto bisa zargin bai iya soyayya ba. Matar tace tunda suka yi aure ko kiss Mijin nata bai taba mata ba, da yayi Niyyar kwanciyar aure da ita saidai kawai yace mata ta bude masa. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1938153791884562726?t=WKQilKs5FLBd9-R5ELA4jg&s=19 Menene ra'ayinku aka wannan?
Duk me Tambayar me aka yi da kudin Tallafin man fetur, ya zo jihar Nasarawa ya gani>>Inji Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule

Duk me Tambayar me aka yi da kudin Tallafin man fetur, ya zo jihar Nasarawa ya gani>>Inji Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule

Duk Labarai
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya bayyana cewa masu tambayar ya aka yi da kudin tallafin man fetur su zo jihar Nasarawa su ga yanda aka yi dasu. Ya bayyana hakane a yayin ziyarar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai jihar Nasarawa ta kwanaki daya inda ya samu rakiyar manyan ma'aikatan Gwamnati ciki hadda Gwamnonin APC da dama. Gwamnan yace manya-manyan canje-canjen da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kawo wa Najeriya sune cire tallafin Man fetur sai kuma cire tallafin dala. Ya bayyana cewa kuma duka an shaida irin ci gaban da hakan ya kawo musamman su a jiharsu ta Nasarawan.
A yau zan kafa sabon Tarihin saka hannu a kudirin dokar canja Haraji da zai amfani har wadanda bama a haifa ba>>Shugaba Tinubu

A yau zan kafa sabon Tarihin saka hannu a kudirin dokar canja Haraji da zai amfani har wadanda bama a haifa ba>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, a yau, Alhamis zai kafa sabon Tarihi da Tubalin ci gaban Najeriya wanda zai amfani har ma wadanda ba'a haifa ba. Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta kafar sada zumuntarsa inda yace yana godiya ga 'yan Najeriya bisa hadin kan da suka bashi na canja fasalin Karbar Haraji a Najeriya. Shugaban yace wannan sabon kudirin na Haraji zai habaka kasuwanci a Najeriya sosai domin akwai adalci a cikinsa. Shugaban ya bayyana cewa, yana kira ga 'yan kasuwa na Duniya cewa ga dama ta samu ta zuba hannun jari a Najeriya. Ya kuma godewa, Kwamitin da ya kafa na canja fasalin karbar Harajin da majalisar dattijai da Gwamnatocin jihohi bisa gudummawar da suka bayar wajan tabbatar da canja fasalin karbar Harajin.