Tuesday, December 16
Shadow
Ba dan kìyàyyà ga wasu mutanene yasa aka yi yàkìn basasa ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Ba dan kìyàyyà ga wasu mutanene yasa aka yi yàkìn basasa ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa na mulkin Soja, Janar Yakubu Gowon ya bayyana cewa, ba dan kiyayya ga wasu mutanene yasa aka yi yakin basasa ba a Najeriya. Ya bayyana hakane ranar Asabar a Abuja inda yace dalilai na neman hadin kan kasa ne suka sa dole suka fito aka yi yakin basasa dasu. Yakubu Gowon ya bayyana muhimmancin yafiya, da sasanci da hadin kai. Ya bayyana cewa, ya tuna da lokaci mafi wahala a rayuwarsa, watau lokacin yakin basasa, inda yace abu ne da bashi da zabi akansa, kuma yayi abinda ya kamata dan ganin an hada kan kasarnan. Janar Yakubu Gowon dan shekaru 91 yace shima yayi asara a yakin basasa dan kuwa a yakin basasa ne ya rasa babban abokinsa, Major Arthur Unegbe.
A yayin da Kungiyar Dattawan Yarbawa ta Afenifere take kiran a tsige Shugaba Tinubu saboda bai tsinanawa ‘yan Najeriya komai ba, Kungiyar Matasan Yarbawan sun ce basu yadda a tsige shugaban ba

A yayin da Kungiyar Dattawan Yarbawa ta Afenifere take kiran a tsige Shugaba Tinubu saboda bai tsinanawa ‘yan Najeriya komai ba, Kungiyar Matasan Yarbawan sun ce basu yadda a tsige shugaban ba

Duk Labarai
Kungiyar Matasan Yarbawa, (YYSA) tace bata amince da kiran da kungiyar dattawan Yarbawan ta yi ba na cewa a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda yaudarar 'yan Najeriya. Shugaban kungiyar, Olalekan Hammed ne ya fitar da sanarwar ranar Lahadi inda yace zargin da akewa shugaba Tinubu na baiwa kamfanin Mr. Gilbert Chagoury aikin gina titin Legas zuwa Calabar wanda ke da alaka dashi ba gaskiya bane. Yace kamfanin na da tarihin yin ayyuka masu kyau. Yace kiran a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cike yake da siyasa sannan zargin da ake masa bashi da tushe ballantana makama. Sannan yacw shi Tinubu yana duba cancanta ne kamin ya bayar da aiki.
Mutane 9 sun rasu sanadiyyar hadarin mota a jihar Jigawa

Mutane 9 sun rasu sanadiyyar hadarin mota a jihar Jigawa

Duk Labarai
A kalla Mutane 9 ne suka rasu a hadarin mota da ya faru a kauyen Kyaramma dake karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa. Hukumar 'yansandan jihar ta tabbatar da faruwar hadarin inda tace ya farune da misalin karfe 2 na yamma tsakanin wasu motocin Golf 3 guda biyu wanda kuma ya bar mutane da yawa sun jikkata. Kakakin 'yansandan jihar, Shiisu Adam ne ya bayyana hakan inda yace motocin sun yi taho mu gama, yace bayan hadarin 'yansandan sun kai dauki wajan inda suka kai wadanda suka jikkata Asibiti. Kwamishinan 'yansandan jihar, CP A.T. Abdullahi, ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan mamatan inda yace direbobi su rika kiyaye dokokin hanya dan gujewa hadarin.
Kalli yanda Wani Bayerabe yayi tsalle ya fada Rijiya bayan da ya sha kwaya ranar Sallah Saboda murna

Kalli yanda Wani Bayerabe yayi tsalle ya fada Rijiya bayan da ya sha kwaya ranar Sallah Saboda murna

Duk Labarai
Wani bayerabe ya fada rijiya a garin Ilorin West na jihar Kwara bayan da ya sha kwaya da ake cewa Colorado. Ya sha kwayar ne ranar Sallar, watau Juma'ar data gabata inda tasashi ya haukashe ya tuma ya fada Rijiyar. Sunan mutumin Kareem dan shekaru 43. Hukumar kwana-kwana ta jihar ta bayyana cewa, an kirata aka sanar da ita lamarin da misalin karfe 10:29 na safe, kamar yanda kakakin hukumar, Hassan Adekunle ya bayyana. Yace da suka je sun fitar da gawar mutumin inda suka mikata hannun 'yansanda.
Allah ya gayamin idan na bar cocin RCCG dana na farko zai mùtù>>Inji Fasto Enoch Adeboye

Allah ya gayamin idan na bar cocin RCCG dana na farko zai mùtù>>Inji Fasto Enoch Adeboye

Duk Labarai
Babban Faston cocin RCCG, fasto Enoch Adeboye ya bayyana cewa, Allah ya taba gargadinsa cewa idan ya bar cocin RCCG din dansa na farko zai mutu. Faston ya bayyana hakane a wajan wani taron addu'a da aka yi a cocinsa ta RCCG din dake Ogun ranar 7 ga watan Yuni. Faston ya bayyana damuwa sosai kan yanda wasu kiristoci ke tsalle daga wannan coci zuwa wancan coci. Inda yace shi kam Allah ne ya hanashi canja coci dan ya gargadeshi idan ya canja, dansa na fari zai mutum.
Kalli Bidiyo: In baka da Miliyan 50 ba zan iya auren ka ba>>Inji Wannan matashiyar

Kalli Bidiyo: In baka da Miliyan 50 ba zan iya auren ka ba>>Inji Wannan matashiyar

Duk Labarai
Wata matashiya ta dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da tace idan mutum bashi da Miliyan 50 ba zata iya aurensa ba. Ta bayyana hakane a wani shirin da ake hira da ita. Tace miliyan 50 din da take magana ba wai na wani abu bane, na shagalin bikine take magana akai. https://www.tiktok.com/@juicy_lifstyle/video/7512539700184337670?_t=ZM-8x1x4TwvWGW&_r=1 Da yawa dai sun bayyana mamaki da wannan ikirari nata.
Karanta Jadawalin Fitattun ‘Yan Siyasa Goma Da Suka Fi Kowanne Dan Siyasa Kudi A Nijeriya

Karanta Jadawalin Fitattun ‘Yan Siyasa Goma Da Suka Fi Kowanne Dan Siyasa Kudi A Nijeriya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Fitattun 'Yan Siyasa Goma Da Suka Fi Kowanne Dan Siyasa Kudi A Nijeriya Bola Ahmed Tinubu Ibrahim Badamasi Babangida Orji Uzor Kalu Andy Uba Abubakar Bukola Saraki David Mark Ifeanyi Ubah Olusegun Obasanjo Atiku Abubakar Rochas Okorocha Me za ku ce? MAJIYA: Politics Nigeria
Ku bi duk inda masu yiwa Najeriya barazanar tsaro suke ku gama dasu>>Shugaban Sojojin Najeriya ya baiwa sojojin Umarni

Ku bi duk inda masu yiwa Najeriya barazanar tsaro suke ku gama dasu>>Shugaban Sojojin Najeriya ya baiwa sojojin Umarni

Duk Labarai
Shugaban sojojin Najeriya, COAS, Lt.-Gen. Olufemi Oluyede ya baiwa sojojin Umarnin su bi duk inda masu yiwa Najeriya barazanar tsaro suke su gama dasu. Ya bayar da wannan umarnin ne a yayin bikin sallah tare da sojojin a Giwa dake jihar Kaduna. Maj.-Gen. Erema Akerejola, ne ya wakilci shugaban sojojin a wajan bikin sallar. Yace biyayya da karfin hali da sojojin Najeriya ke nunawa ya taimaka matuka wajan nasarorin sa suke samu a fagen daga. Ya kuma jinjinawa sojojin da suka rasa rayukansu a fagen daga inda yace yana baiwa iyalansu tabbacin jajircewar da suka nuna ba zata tafi a banza ba.
Kasar Ìran ta yiwa kasar Israyla mummunan kutse inda ta kwashi bayananta game da makamin kare danginta

Kasar Ìran ta yiwa kasar Israyla mummunan kutse inda ta kwashi bayananta game da makamin kare danginta

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Iran na cewa, kasar ta yiwa kasar Israyla kutse inda ta kwashi bayananta game da makamashin kare danginta. Rahoton yace kasar Iran ta dauki hayar wasu 'yan kasar Israelan aiki ne inda ta rika biyansu makudan kudade wanda suka rika bata bayanan sirri game da kasar ta Israela. Iran ta sanar da cewa ta dade tana wannan shirin kuma ba yau ta yi nasara ba amma dai ta tsaya ne kamin ta tabbatar da takardun bayanan sirrin kasar Israelan sun zo hannunta kamin ta sanar da nasarar ta. Kasar Israyla dai bata ce uffan ba kan lamarin. Saidai wasu rahotanni sun ce an kama wasu mutane da ake zargin sun hada kai da kasar Iran a cikin kasar ta Israela. A shekarun baya dai, kasar Israela itama tawa kasar Iran irin wannan kutse.
SANARWA GA MATAFIYA: Yanzu Haka Hanyar Abuja Zuwa Kano-Kaduna Ta Cunkushe, Inda Masu Ababen Hawa Suka Yi Curko-Curko Dauke Da Matafiya Musamman Masu Zuwa Hidimar Sallah

SANARWA GA MATAFIYA: Yanzu Haka Hanyar Abuja Zuwa Kano-Kaduna Ta Cunkushe, Inda Masu Ababen Hawa Suka Yi Curko-Curko Dauke Da Matafiya Musamman Masu Zuwa Hidimar Sallah

Duk Labarai
SANARWA GA MATAFIYA: Yanzu Haka Hanyar Abuja Zuwa Kano-Kaduna Ta Cunkushe, Inda Masu Ababen Hawa Suka Yi Curko-Curko Dauke Da Matafiya Musamman Masu Zuwa Hidimar Sallah. Idan da wata hanya da matafiya masu bin hanyar za su bi, gwamma su sauya don gudun fadawa cikin cunkuson. Wasu rahotonnni da Rariya ta samu, sun bayyana cewa cunkoson motocib ba ya rasa na nasaba da gyaran hanya da ake yi. Jama'a don Allah a yada (sharing) domin amfanar matafiyan dake shirin bin hanyar.