Saturday, December 20
Shadow
Ka Daina Boye-Boye Ka Fito Fili Ka Koma Jam’iyyar APC, Matawalle Ga Gwamnan Zamfara

Ka Daina Boye-Boye Ka Fito Fili Ka Koma Jam’iyyar APC, Matawalle Ga Gwamnan Zamfara

Duk Labarai
Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Dr. Bello Mohammed Matawalle, ya bukaci Gwamna mai ci, Dr. Dauda Lawal, da ya fito fili ya bayyana cewa ya shiga jam’iyyar APC ya daina wani boye-boye. Da yake jawabi a gidansa da ke Maradun yayin wata ziyarar gaisuwar Sallah da dubban magoya baya suka kai masa, Matawalle ya ce lokaci ya yi da Gwamna Lawal zai daina “kumbiya-kumbiya" yana rufa-rufa” ya fito fili ya bayyana matsayarsa a jam'iyyance. “Kofar jam’iyyarmu a bude take ga duk wanda ke neman ci gaban gaskiya ga jihar Zamfara da Nijeriya,” inji Matawalle, yana mai jaddada cewa bai dauki komai a ransa ba dangane da zabin siyasar Gwamna Lawal. Ya ce APC jam’iyya ce da ke kan turbar tawali’u, gaskiya da shugabanci nagari. “Muna kira gare shi ya ...
‘Idan ba a yashe Alo Dam ba za mu iya fuskantar matsala a Borno’

‘Idan ba a yashe Alo Dam ba za mu iya fuskantar matsala a Borno’

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Borno ta yi kira ga gwamnatin shugaba Tinubu ta hanzarta daukar mataki kan ɗan kwangilar da ta baiwa aikin yashe dam din Alou da ya haifar da ambaliya a bara. Ta ce duk da cewar sun yashe wani sashe na dam din amma, har yanzu akwai babbar barazana da za a iya fuskantar mumunar ambaliya. Kwamishinan yaɗ labarai da harkokin tsaro na jihar Borno, Farfesa Umar Tar da harkkokin tsaro ya shaida wa BBC cewa an bayar da kwantaragin kuma minista ya je ya ƙaddamar da aikin. "Har yanzu ba mu ga ƴan kwangila sun zo domin fara aikin ba kuma yanzu ga damuna ta riga ta sauka. Idan ba a yi aikin nan da wuri ba to idan ruwa ya zo ya yi halinsa to lallai za a samu matsala. Ya kamata ace an yashe ruwan saboda irin cunkushewar da ya yi. Idan aka yashe shi to ko ruwa ya zo da yawa ba z...
Ƴansanda sun kama mutum 27, sun ƙwàtò màggàn màkàmài a Kaduna

Ƴansanda sun kama mutum 27, sun ƙwàtò màggàn màkàmài a Kaduna

Duk Labarai
Ƴansanda a jihar Kaduna sun ce sun kama mutum 27 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daba-daban. Wata sanarwar da mai magana da yawun ƴansandan jihar DSP Mansir Hassan ya fitar, ta ce an samu nasarar kama ɓata-garin ne bayan wani samame da ta kai maɓoyarsu a yankin Kawo. "Mun kai samamen ne jiya Lahadi a lungu da sako na yankin Kawo. Abin ya kai ga kama mutum 27 da ake zargi da aikata laifuka har ma da ƙwato muggan makamai," in ji Mansir. Ya ce cikin makaman da suka ƙwato sun haɗa da wuƙaƙe da adduna da fartanyu da kuma ƙunshin ganyayyaki da ake kyautata zaton tabar wiwi ce da kuma sauran kayan maye. Kwamishinan ƴansandan jihar, CP Rabiu Muhammad ya ƙara nanata ƙoƙarin rundunar wajen ganin an mutunta doka da oda a faɗin jihar. Ya ƙara da cewa Kaduna jiha ce mai zaman lafiya,...
Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2027, Peter Obi ya bayyana cewa, babu Dimokradiyya a mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana cewa idan aka lura da abinda ya faru a jihar Rivers da zaben jihar Edo za'a iya gane cewa, babu Dimokradiyya a Najeriya. Peter Obi ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi a Arise TV. Yace shiyasa yake ta neman ya zama shugaban kasa, saboda ya gyara wannan matsalar, yace a kaf cikin masu neman takarar shugaban kasar, babu gwani wanda ke da kwarewa kamarsa saboda yayi aiki da kamfanoni kuma ya zama gwamna.
Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Kakakin jam'iyyar PDP a jihar Legas, Hakeem Amode ya koma jam'iyyar APC. Ya bayyana hakane a wata ganawa da manema labarai tare da masoyansa a Ikeja ranar Litinin. Sun bayyana cewa, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na jihar, Abdul-Azeez Adediran (Jandor), da ya koma APC ne ya dauki hankulansu suka koma jam'iyyar APC. A jawabinsa yace duka jam'iyyar PDP a jihar daga sama har kasa sun koma APC inda yace saboda jam'iyyar PDP ta tasa alkibla.
An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

Duk Labarai
Kungiyar masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun kaddamar da shafin yanar gizo na wadanda kw da ra'ayin sake zaben shugaban kasar a shekarar 2027. Kungiyar me suna the BAT Ideological Group ta bayyana cewa, ta yi hakanne dan hada bayanan masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da wanda suke son sake zabensa. Kungiyar tace kuma hakan zai saukaka maganar ace sai mutum ya je Abuja dan za'a yi meeting ko dan zai yi rijista. Tace kuma hakan zai saukaka mata yada manufar shugaban kasar ga al'umma. Shugaban kungiyar, Bamidele Atoyebi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, jami'an tsaro a jihar Legas karkashin rundunar RRS dake Falomo a Ikoyi sun kama wani mutum da kwalayen sigari guda 9 da ya sata daga wani babban shagon da ake cewa, Super Market. An kiyas ta cewa darajar kwalayen sigarin da ya sata zasu kai Naira Dubu 90. Hukumar 'yansandan tace ta kama wanda ake zarginne da misalin karfe 5:30 pm na yammacin ranar Labadi. Hukumar 'yansandan tace kowane kwalin sigari ana sayar dashi akan Naira dubu 10 wanda jimulla kudin sigarin da ya sata Naira dubu 90 kenan. Sunce Tuni suka mikashi ga hukumar 'yansanda ta Falomo.
Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume daga jihar Borno ya bayyana cewa, karya ake masa shi baice an kaiwa tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai hari ba. Rahotanni sun watsu cewa, Sanata Ali Ndume ya ce an kaiwa Buratai hari a ranar Juma'ar data gabata inda ya tsallake rijiya da baya. Saidai a bayanin Sanata Ali Ndume bayan da wancan labari ya watsu shine shi bai ce haka ba, cewa yayi an kaiwa garin Buratai hari ne ba tsohon shugaban sojojin ba. Mayakan kungiyar dake ikirarin Jìhàdì ta Bòkò Hàràm dai sun dawo gadan-gadan inda suke kaiwa jami'an tsaro hare-hare akai-akai inda wasu rahotannin ke cewa ma sun fi sojojin Najeriya makaman yaki.
Duk da karin kudin wutar Lantarki da kamfanonin wutar Najeriya suka yi, aun tafka Asara

Duk da karin kudin wutar Lantarki da kamfanonin wutar Najeriya suka yi, aun tafka Asara

Duk Labarai
Kamfanonin rarraba wutar Lantarki na Najeriya Discos sun bayyana cewa, sun tafka asarar Naira Biliyan N202bn a watanni 3 na farkon shekarar 2025. Hakan na zuwane duk da kara kudin wutar da kamfanonin Discos din suka yi. Rahoton yace an yi karin kudin wutar da kaso 106.68 cikin 100. Rahoton yace kamfanonin wutar Lantarkin da ake dasu guda 12 sun aikawa da mutane bill din wuta na Naira Biliyan N761.91bn a tsakanin watan Janairu zuwa Maris. Saidai naira Biliyan N559.3bn ce kwastomomin suka iya biya a matsayin kudin wutar. Hakan na nufin ba'a biya Naira Biliyan N202.61bn na kudin wutar. Idan aka kwatanta da shekarar 2024, inda kamfanonin wutar suka aikawa kwastomomin bill din Naira Biliyan N368.65bn amma suka karbi Naira Biliyan N291.62bn, basu karbi Naira Biliyan N77.03bn ba...
Hadimin Shugaba Tinubu, Aliyu Audu ya ajiye mukaminsa, shine na 3 da ya ajiye mukaminsa a mulkin Tinubu

Hadimin Shugaba Tinubu, Aliyu Audu ya ajiye mukaminsa, shine na 3 da ya ajiye mukaminsa a mulkin Tinubu

Duk Labarai
Hadimin shugaban kasa, me bashi shawara akan harkar jama'a, Aliyu Audu ya ajiye aikinsa na baiwa shugaban kasar ahawara. Ya bayyana hakane a sakon da ya aikawa shugaban kasar a cikin wasika ranar 8 ga watan Yuni inda yace yana godiya matuka da damar da shugaban kasar ya bashi na bautawa kasarsa. Ya yabawa tsohon hadimin shugaban kasar, Ajuri Ngilale wanda yace ta sanadiyyarsa ne ya samu wannan mukami. Shima dai Ajuri Ngilale ajiye mukaminsa yayi daga Gwamnatin Tinubu. Hakanan bayanshi, akwai Hakeem Baba Ahmad da shima ya ajiye mukamin nasa.