Friday, December 5
Shadow
Allah Sarki: Karanta Jadawalin Manyan Sojojin da suka rhasa Rhayuwkansu a Fagen daga

Allah Sarki: Karanta Jadawalin Manyan Sojojin da suka rhasa Rhayuwkansu a Fagen daga

Duk Labarai
A ranar Talata ne rahotonni suka fara ɓulla cewa mayaƙan ƙungiyar Islamic State of West Africa Province (Iswap) ta kashe Birgediya Janar Musa Uba a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya. Kisan nasa ya tayar da muhawara game da yadda ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi kamar Boko Haram da Iswap ke kashe manyan jami'an sojin Najeriya, duk da cewa ba shi ne na farko da ya mutu a filin daga ba. Bayanai sun nuna cewa Janar Uba ne babban jami'i na biyu mafi girman muƙami da 'yanbindigar suka kashe tun shekarar 2021. Iswap ta bayar da sanarwar kisansa a shafinta na Telegram, inda ta ce mayaƙanta sun kama shi ranar 15 ga watan Nuwamba bayan harin kwanton-ɓauna da suka kai wa sojojin Najeriya a kusa da garin Wajiroko da ke jihar ta Borno. Rundunar sojan Najeriya ta tabbatar da kai h...
Rahoto: Rashin aikin yi a tsakanin Matasan Qasar Amurka yayi Qamari, babu banbanci tsakanin masu Digiri da wadanda basu je makaranta ba

Rahoto: Rashin aikin yi a tsakanin Matasan Qasar Amurka yayi Qamari, babu banbanci tsakanin masu Digiri da wadanda basu je makaranta ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Rashin aikin yi a tsakanin matasan kasar Amurka yayi Qamari. Rahoton wanda gidan jaridar Fortune ya wallafa yace a tsakanin matasa masu shekaru tsakanin 22 zuwa 27, rashin aikin yin su iri daya ne, babu banbanci tsakanin wanda yaje makaranta da wanda bai kammala Digiri ba. Rahoton yace rashin aikin yi a tsakanin matasan ya kai makin kaso 5.5 cikin 100. Rahoton yace kamfanoni da yawa da masu daukar aiki sun rage baiwa kwalin Digiri muhimmanci. Hakan yasa matasa suka fara barin karatun Digiri suna komawa makarantun koyon sana'a.
Doka ta bani dama zan iya kwace fili daga hannu kowanene sannan in baiwa wanda nake so a Abuja>>Inji Wike

Doka ta bani dama zan iya kwace fili daga hannu kowanene sannan in baiwa wanda nake so a Abuja>>Inji Wike

Duk Labarai
Ministan Babbban Birnin Tarayya, Abuja Nyesom Wike ya bayyana cewa, doka ta bashi damar kwacewa da baiwa kowa yake so fili. Ya bayyana hakane yayin ziyarar da shuwagabannin hukumar kula da yankin kudu maso kudu suka kai masa. Yace idan mutum ya bar filinsa ba tare da ginawa ba na tsawon lokaci, ko kuma ya ki biyan haraji ko ya saba doka zai iya kwace filinsa. Wike yace baya kwace fili saboda siyasa yace abin takaici ne ace mutane basa son biyan Haraji amma suna son gwamnati ta rika musu aikin gina kasa.
Kalli Bidiyo: Amsar da Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Zeezee ta bauwa wani da yace mata Timaya ya hama Qakuleta

Kalli Bidiyo: Amsar da Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Zeezee ta bauwa wani da yace mata Timaya ya hama Qakuleta

Duk Labarai
Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Ummi Zeezee ta wallafa Bidiyo a shafinta na Tiktok tana sauraren wakar Aliya inda anan ne wani ya bayyana cewa Timaya ya gama kwakuleta. Saidai maimakon ta ji haushi, Ummi ta gaya masa cewa, zaka maimaita Ranar Sakamko ai. https://www.tiktok.com/@ummi_zee_zee_offi/video/7573076778344828167?_t=ZS-91XCE153d3Z&_r=1 Ummi Zeezee dai ta yi soyayya da mawakin Kudu, Timaya wanda a wancan shekarun lamarin ya jawo cece-kuce.
Kalli Bidiyon yanda matashi ya fito yana zanga-zanga shi kadai yana kiran kasar Amurka ta kawo dauki Najeriya inda yace shuwagabanni sun gaza

Kalli Bidiyon yanda matashi ya fito yana zanga-zanga shi kadai yana kiran kasar Amurka ta kawo dauki Najeriya inda yace shuwagabanni sun gaza

Duk Labarai
Wani matashi kenan da ya fito a Abuja yana zanga-zanga shi kadai yana cewa, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya kawo dauki Najeriya. An ga matashin a Bidiyo yana daga kwali yana durkusawa kasa yana kiran sunan Trump. https://www.tiktok.com/@gabriel__timothy/video/7574103452331134216?_t=ZS-91XAQO7iV8K&_r=1
An gano cewa, Wasu Inyamurai ne masu son kafa kasarsu suka kai Rahoton cewa ana Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya zuwa kasar Amurka

An gano cewa, Wasu Inyamurai ne masu son kafa kasarsu suka kai Rahoton cewa ana Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya zuwa kasar Amurka

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wasu Inyamurai ne karkashin wata Kungiya ta son kafa kasar Biafra suka kai kara kasar Amurka cewa ana yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi a Najeriya. Rahoton yace kungiyar me suna the United States of Biafra da sauran wasu kungiyoyin dake karkashinta sun mika wannan korafi ne ga Hukumar FARA ta kasar Amurka. Sannan Sanatan kasar Amurka, Ted Cruz ya taimaka musu wajan yayata wannan magana inda yace babu inda akewa Kiristoci Khisan kyiyashi kamar a Najeriya. Lamarin dai ya watsu sosai musamman a kafafen sada zumunta. Saidai Tuni Gwamnati ta musanta wannan rade-radin.
Duk Duniya babu Kabilar dake saka Addini sama da Kabilarta sai Hausawa, Muddin Muna son ci gaba a Arewa, sai mun raba gari da Fulani da Larabawa>>Inji Isa Bako

Duk Duniya babu Kabilar dake saka Addini sama da Kabilarta sai Hausawa, Muddin Muna son ci gaba a Arewa, sai mun raba gari da Fulani da Larabawa>>Inji Isa Bako

Duk Labarai
Bahaushe dake zaune a kasar Amurka, Isa bako ya bayyana cewa, Duk Duniya babu wanda ke saka Addini sama da Kabilarsa sai Bahaushe. Ya bayyana cewa idan ana son ci gaba a Arewa, sai Hausawa sun raba gari da Fulani da kuma Larabawa. Yace Hausawa sun fi kusa da Inyamurai fiye da Fulani da Larabawa. https://www.tiktok.com/@isa.bako4/video/7573651068588985655?_t=ZS-91X2GqODUOm&_r=1
Da Duminsa: Tinubu ya ɗage tafiyar sa don Alhinin Daliban jihar Kebbi

Da Duminsa: Tinubu ya ɗage tafiyar sa don Alhinin Daliban jihar Kebbi

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ɗage tafiyar da ya shirya yi a yau zuwa Afirka ta kudu da kuma Angola, a yayin da ya ke jiran sauraron rahoto game da sace ɗalibai da aka yi a Kebbi da harin da aka kai kan wani coci a Kwara. A cikin wata sanarwa da mai magana da yauwansa, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaban ya umurci a aika ƙarin jam'ian tsaro karamar hukumar Ekiti da ke jihar Kwara inda lamarin ya faru kamar yadda gwamnan jihar ya buƙata, tare kuma da bai wa ƴansanda umurnin farauto ƴan bindigar da suka kai hari kan masu ibadar. A yau Laraba ne shugaban ya tsara barin ƙasar domin halartar taron shugabannin ƙasashe ashirin masu ƙarfin tattalin arziƙi (G20) karo na ashirin da za a yi a Afirka ta Kudu, daga nan kuma zai ƙarasa Luanda da ke Angola domin halartar karo na bakwai na taro...