Tuesday, December 23
Shadow
Real Madrid ta sanar da ɗaukar Alonso a matsayin sabon kocinta

Real Madrid ta sanar da ɗaukar Alonso a matsayin sabon kocinta

Duk Labarai
Real Madrid ta sanar da ɗaukar Xabi Alonso a matsayin sabon kocinta. Alonso wanda ya buga wa Real ɗin wasa 236 a matsayin ɗan wasanta a baya, ya saka hannu kan kwantiragin shekara uku. A farkon watan nan ne ya sanar da cewa zai bar Bayer Leverkusen da yake jagoranta. Tsohon ɗan wasan na Liverpool da kuma Sifaniya, ya jagoranci ƙungiyar lashe kofin Bundesliga a bara ba tare da an doke shi ko da wasa ɗaya ba - da kuma German Cup. Alonso wanda yarjejeniyarsa za ta kai har 30 ga watan Yunin 2028, zai maye gurbin Carlo Ancelotti. Ancelotti ya jagoranci wasansa na karshe a Madrid a ranar Asabar, inda a yanzu zai zama sabon kocin ƙasar Brazil. Za a gabatar da Alonso wanda ya lashe Champions League a 2014 lokacin da yake buga wa Madrid kwallo - a gobe Litinin a filin atisayen ƙun...
‘Yadda tsohon mijina ya sake ni bayan ƙwace min kwangilar biliyoyin naira’

‘Yadda tsohon mijina ya sake ni bayan ƙwace min kwangilar biliyoyin naira’

Duk Labarai
Fitacciyar jaruma a Masana'antar Kannywood, Masurah Isah ta tabbatar da mutuwar aurenta na biyu, wanda ta bayyana cewa ya zo mata a wani yanayi na ba-zata, kamar almara. Mansurah ta ce ita aure ta yi na soyayya, domin a cewarta, "so makaho nr", amma ashe mijin da wata manufar daban ya zo, ba aure na gaskiya ba. Mansurah ta bayyana haka ne a shirin Mahangar Zamani na BBC Hausa, inda BBC ta tattauna da ita tare da tsohuwar jaruma a masana'antar, Fati Mohammad kan zargin matan Kannywood da rashin zaman aure. Da take shimfiɗa, Fati Mohammad ta ce mutane ne suke musu gurguwar fahimta, domin "shi aure ai yana da rai, kuma idan Allah ya kawo ƙarshensa, dole sai ya ƙare. Mutane da yawa aurensu yana mutuwa, amma saboda ba a sansu ba, sai ba za a ji ba," in ji ta. Ta ce yawanci...
Tun ba’a je ko ina ba, Riciki ya kunno kai a jam’iyyar ADC da su Atiku da Peter Obi ke son komawa dan kwace mulki a shekarar 2027

Tun ba’a je ko ina ba, Riciki ya kunno kai a jam’iyyar ADC da su Atiku da Peter Obi ke son komawa dan kwace mulki a shekarar 2027

Duk Labarai
Rahotanni na cewa, riciki ya kunno kai a jam'iyyar ADC da su Atiku da Peter Obi ke son amfani da ita dan tsayawa takarar sugaban kasa a shekarar 2027. Rahotanni sun ce jam'iyyar a asirce ta canja kundin tsarin mulkinta inda ta baiwa sabbi da tsaffin membobinta dama iri daya, ana tunanin ta yi hakanne saboda manyan 'yan siyasa irin su Atiku dake shirin komawa cikinta. Saidai wasu tsaffin 'yan jam'iyyar sun ki amincewa da wannan mataki inda suka ce ba zasu baiwa kowa mukaman sa suke rike dashi ba musamman wadanda suka shiga jam'iyyar daga baya. Saidai wasu 'yan jam'iyyar wanda basu da yawa sun amince da wannan mataki. Ana tunanin 'yan Jam'iyyar Adawa zasu yi amfani da jam'iyyar ADC dan yakar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a shekara 2027.
Hankula sun tashi bayan da aka dauke wutar lantarki a kasar Faransa na tsawon awanni 5

Hankula sun tashi bayan da aka dauke wutar lantarki a kasar Faransa na tsawon awanni 5

Duk Labarai
Rahotanni daga birnin Riviera na kasar Faransa inda ake bikin fina-finai na kasa da kasa na cewa, an dauke wuta na tsawon akalla awanni 5. Hakan ya kawo tarnaki a bikin finafinan da ake yi inda baki da dama da suka je wajan bikin ke kokawa musamman game da maganar kudi da zasu yi hidima dasu saboda bankuna da ATM duk sun samu tangarda saboda rashin wutar. Rahotanni sun ce wasu bata garine suka lalata kadarorin wutar lantarkin wanda hakan ya kawo tarnaki aka dauke wutar. Lamarin ya zowa mutane da mamaki ganin kasa me ci gaba irin Faransa ta samu matsalar wutar lantarki haka.
ASUU ta yi barazanar tafiya yajin aiki da rufe jami’o’in Najeriya

ASUU ta yi barazanar tafiya yajin aiki da rufe jami’o’in Najeriya

Duk Labarai
Ƙungiyar malaman jami'o'in Najeriya ASUU ta yi kira ga gwamnatin ƙasar da ta cika yarjejeniyar da suka shiga a shekarar 2009 ko ta tsunduma yajin aiki. Shugaban ASUU, Chris Piwuna ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a ranar Juma'a a Abuja. Ya nanata buƙatar da ke akwai na gwamnatin ta cika yarjejeniyar da alƙawuran da ta ɗauka domin magance matsalolin da jami'o'in ƙasar ke fuskanta. Piwuna ya ce har yanzu akwai wasu muhimman batutuwa guda tara da ba a daddale su ba a yarjejeniyar da suka shiga. Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi yana cewa daga cikin abubuwan da suka rage akwai albashin malaman da ba a biya ba lokacin da suke yajin aiki na shekarar 2022 da wasu alawus ɗinsu da ake riƙe saboda IPPIS da sauransu. Ya ce duk da alƙawarin da gwamnati ta yi na zuba...
Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwa game da yanda ake kirkiro Bidiyo na bogi na shugaban kasa dake nunashi a wani yanayi mara kyau domin ɓata masa suna

Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwa game da yanda ake kirkiro Bidiyo na bogi na shugaban kasa dake nunashi a wani yanayi mara kyau domin ɓata masa suna

Duk Labarai
Ministan yaɗa labaran Najeriya Mohammed Idris ya gargaɗi ƴan ƙasar kan amfani da ƙirƙirarrun bidiyo domin nuna shugabannin ƙasar a wani yanayi mara kyau domin ɓata musu suna. Jaridar The Nation mai zaman kanta ta ruwaito ministan yana cewa, "mun ga yadda ake amfani da ƙirƙirarriyar basira ta hanyoyin da suka dace, da hanyoyin da ba su dace ba. Zai iya yiwuwa kana zaune a nan kawai sai wani ya yanko kanka ya ɗaura a wani jikin domin ɓata maka suna." "Muna ganin yadda ake juya maganar shugaban ƙasa, inda zai faɗa abu daban, amma sai a canja abin da ya faɗa. Ko kuma minista ya faɗa wani abu, sai a juya masa magana," in ji shi. Ya ƙara da cewa suna duba lamarin sosai a matakin gwamnati, "musamman yadda za mu tsaftace kafofin sadarwa ba tare da tauye haƙƙin furta albarkacin baki ba."...
Mun ba ɗaliban Najeriya rancen naira biliyan 56.85 a shekara ɗaya – Gwamnatin Tarayya

Mun ba ɗaliban Najeriya rancen naira biliyan 56.85 a shekara ɗaya – Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Hukumar Bayar da Bashin Karatu ta Najeriya Nelfund ta ce ta ba ɗaliban Najeriya rancen kuɗi naira biliyan 56.55 domin biyan kuɗin makaranta da alawus ɗin kashewa na yau da kullum. Hukumar ta bayyana haka ne domin bayyana nasarorin da ta samu a cikin shekara ɗaya da fara aiki tun bayan ƙirƙirar shirin. A wata sanarwa da daraktan sadarwa na hukumar, Oseyemi Oluwatuyi ta fitar, ya ce sama da ɗalibai 600,000 ne suke nami rancen, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. "Bayan tantancewa, mun amince tare da ba ɗalibai 550,000 rancen, inda muka ba su kuɗi naira biliyan 56.85 a cikin shekara guda." "Tsarin bayar da rancen ya taimaka wajen sauƙaƙa wa ɗaliban Najeriya da iyaye," in ji ta.
Tinubu Akwai Zalamar Mulki, Yanzu duk wahalar rayuwa da matsalar tsaro da sauransu da ‘yan Najeriya ke ciki bai dameshi ba, zarcewa akan kujerar mulki ce a gabanashi? Inji Jam’iyyar PRP

Tinubu Akwai Zalamar Mulki, Yanzu duk wahalar rayuwa da matsalar tsaro da sauransu da ‘yan Najeriya ke ciki bai dameshi ba, zarcewa akan kujerar mulki ce a gabanashi? Inji Jam’iyyar PRP

Duk Labarai
Daya daga cikin jam'iyyun adawa a Najeriya wato PRP, ta yi alawadai da amincewar da kwamitin zartarwa na kasa na jam'iyyar APC mai mulki, da gwamnonin jam'iyyar, da 'yan majalisar dokoki na kasa na jam'iyyar da sauran masu ruwa da tsaki suka yi wa shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu, domin ya sake tsayawa takarar zaben shugaban kasa a shekara ta 2027. Jam'iyyar PRP ta bayyana fargabar, cewa wannan mataki wata zalamar mulki ce kawai, wadda ta fayyace aniyar jam'iyyar APC ta neman ci gaba da mulki karfi da yaji ta hanyar wani goyon baya na musamman da aka tsara, maimakon a bari jama'ar kasa su bayyana ra'ayinsu game da takarar shugaban kasar a zaben da ke tafe. Kwamred Muhammed Ishak, shi ne sakataren watsa labarai na kasa na jam'iyyar PRP, ya shaida wa BBC cewa sanin kowa ne ba wani dad...
Mutanen mu basu da wayau, kudi ake basu suna zaben gurbatattun shuwagabanni>>Inji Dan siyasar jihar Ekiti

Mutanen mu basu da wayau, kudi ake basu suna zaben gurbatattun shuwagabanni>>Inji Dan siyasar jihar Ekiti

Duk Labarai
Dan siyasar jihar Ekiti wanda kuma dan uwa ne ga tsohon gwamnan jihar, Isaac Fayose ya caccaki mutanen jiharsa. Ya bayyana su da marasa wayau inda yace ana basu kudi kalilan suna zaben gurbatattun 'yan siyasa. Yace bayan zabe haka zaka ga sun koma mabarata. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1925900839316574614?t=IFhtaDTEjlrZw-n1W-tH4w&s=19 Maganar tashi ta jawo cece-kuce sosai inda mutanen jihar suka bayyana rashin jin dadinsu, saidai yace shi har yanzu yana nan kan bakarsa.