Tuesday, December 16
Shadow
Yanzu-Yanzu: Bàm ya fashe a Dogon Waya kan titin  Damboa-Maiduguri

Yanzu-Yanzu: Bàm ya fashe a Dogon Waya kan titin Damboa-Maiduguri

Duk Labarai
Rahotanni da muke samu na cewa Bam ya fashe a Dogon Waya kusa da Maiduguri dake kan titin Damboa zuwa Maiduguri. Bam din ya kashe Wani fashinjan motar wanda namiji ne sai kuma Direban motar da wata mata sun jikkata. Direban na dauke da Tumaki ne da yawa wadanda suka sun mutu, kamar yanda kafar Malik Samuel ta Ruwaito. https://twitter.com/Sazedek/status/1921934917950230765?t=rhAXbmg8y1JjXieC9Snytw&s=19 Allah ya kyauta.
Dan majalisar dokokin jihar Kano ya fice daga NNPP zuwa APC

Dan majalisar dokokin jihar Kano ya fice daga NNPP zuwa APC

Duk Labarai
Dan majalisar dokokin jihar Kano ya fice daga NNPP zuwa APC. Dan majalisar dokoki ta jihar Kano mai wakiltar mazabar Sumaila, Hon. Zubairu Hamza Masu, ya fice daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC. A cikin wata wasikar murabus da ya aike wa Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Ismail Falgore, Hon. Masu ya bayyana rikice-rikicen cikin gida da shari'o’in da suka addabi NNPP a matsayin babban dalilinsa na barin jam’iyyar. Kakakin Majalisar, wanda ya karanta wasikar a zauren majalisar yayin zaman ranar Litinin, ya sanar da murabus din Masu daga jam’iyyar tun daga ranar 12 ga Mayu, 2025, tare da tabbatar da cikakken biyayyarsa ga jagorancin jam’iyyar APC daga matakin mazaba har zuwa jiha da kasa baki daya. Dan majalisar ya kara da cewa wasu mutane da dama daga matakin jiha da na kasa su...
Kalli Hoto: An ga gawar wata Budurwa da aka kàshè aka yanke mata al’au7ra

Kalli Hoto: An ga gawar wata Budurwa da aka kàshè aka yanke mata al’au7ra

Duk Labarai
Mutanen garin Abeokuta jihar Ogun sun tashi da wani abin mamaki inda aka ga gawar wata mata akan titin OGTV. An gano cewa bayan kasheta an kuma yanke mata al'aura. Lamarin ya farune ranar Talata inda tuni aka kaiwa 'yansanda korafi. Ba'a dai gano wanda suka yi wannan aika-aika ba amma an yi amannar cewa tsafi ne suke son yi musamman da al'aurarta da suka cire. Tuni aka kai gawarta Mutuware.
Shugaban kasar Korea ta Arewa ya aikewa da matashin shugaban kasar Burkina Faso, Ibrahim Traore da sojoji su bashi kariya bayan da aka yi yunkurin hambarar dashi

Shugaban kasar Korea ta Arewa ya aikewa da matashin shugaban kasar Burkina Faso, Ibrahim Traore da sojoji su bashi kariya bayan da aka yi yunkurin hambarar dashi

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Burkina Faso na cewa, shugaban kasar Korea ta Arewa, Kim Jong un ya aikewa da shugaban kasar, Ibrahim Traore da sojoji dan su bashi kariya. Hakan na zuwane bayan da aka yi yunkurin kifar da gwamnatinsa inda wasu rahotanni suka ce an baiwa hadiman Shugaba Traore makudan kudade su hambarar dashi amma suka kiya.
Kalli Kwalliyar da Rahama Sadau ta yi zuwa wajan Bikin Rarara

Kalli Kwalliyar da Rahama Sadau ta yi zuwa wajan Bikin Rarara

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraruwar fina-finan Hausa, Rahama Sadau kenan a wadannan hotunan nata data sha kwalliya wadda da itace ta je wajan bikin Rarara da A'ishahumaira.
Ana kiran EFCC ta kama Tubabben tsageran Niger Delta, Tampolo bayan da aka ganshi yana wulakanta takardar Naira idan dai ba Talakawa kadai ake kamawa ba

Ana kiran EFCC ta kama Tubabben tsageran Niger Delta, Tampolo bayan da aka ganshi yana wulakanta takardar Naira idan dai ba Talakawa kadai ake kamawa ba

Duk Labarai
Jama'a na ta kira a kama Tubabben tsageran Niger Delta, Tampolo bayan ganinsa yana wulakanta takardar Naira. Da yawa sun kira EFCC ta kama Tampolo ta hukuntashi indai ba talakawa kadai ake hukuntawa ba idan sun wulakanta takardar Nairar. A baya dai EFCC ta kama mutane irin su Murja Kunya, Bobrisky da sauransu inda ake zarginsu da wulakanta Naira.
Jami’ar MAAUN ta rufe gidajen kwanan ɗalibai mata bisa zargin aikata rashin tarbiyya

Jami’ar MAAUN ta rufe gidajen kwanan ɗalibai mata bisa zargin aikata rashin tarbiyya

Duk Labarai
Hukumar gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University of Nigeria (MAAUN) ta ba da umarnin gaggawa na rufewa tare da janye amincewa da gidajen kwanan dalibai mata na Al-Ansar Indabo da ke Hotoro da titin UDB a birnin Kano. Wata sanarwa daga Mataimakin Shugaban Jami’ar mai kula da Rayuwar Dalibai, Dr. Hamza Garba, a ranar Lahadi, ya bayyana cewa wannan matakin rufe gidajen kwanan wani bangare ne na kokarin da jami’ar ke yi domin tabbatar da kwanan dalibai cikin aminci, tsaro da tsafta, da kuma ci gaba da nuna matsayinta na kin yarda da duk wata dabi’a ta lalata daga kowanne ɗalibi. “Na samu umarni daga hukumar gudanarwa na rubuta wannan sako don sanar da iyaye da dalibanmu masu daraja cewa jami’a ta janye amincewarta da GIDAJEN KWANAN DALIBAI MATA NA AL-ANSAR INDABO da ke titin ...
Kalli Bidiyo: Ana zargin shuwagabannin kasashen Faransa, Jamus, da Ingila da shan Hòdàr Iblìs

Kalli Bidiyo: Ana zargin shuwagabannin kasashen Faransa, Jamus, da Ingila da shan Hòdàr Iblìs

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa an ga Shuwagabannin kasashen Faransa, Emmanuel Macron dana Ingila, Sir Keir Starmer da ta jamus, Friedrich Merz suna ta'ammuli da Hòdar Iblìs. https://twitter.com/GlobalDiss/status/1921520024776241239?t=Nlsn9-dGxHwIZqHCW85arg&s=19 Rahoton yace shuwagabannin sun kammala ganawa ne da Shugaban Ukraine, Zelenskyy inda suka shiga jirgin kasa dan komawa kasashen su. https://twitter.com/KevorkAlmassian/status/1921546995900002603?t=YT_ERb4lRgUCAV_W7Y9NJw&s=19 Saidai akan hanyarsu an yi zargin sun shaka hodar Iblis inda har suka manta basu dauke abubuwan da suka yi amfani da su ba akan teburinsu, har wata 'yar Jarida ta shiga wajan da suke ta daukesu hoto. Yar jaridar ta watsa Bidiyon data dauka a kafafen sada zumunta wanda kuma suka dauki ...
Mun tarwatsa sansanin Màhàrà a Borno>>Inji Sojojin Najeriya

Mun tarwatsa sansanin Màhàrà a Borno>>Inji Sojojin Najeriya

Duk Labarai
Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation HADIN KAI (OPHK) sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a wani samame da suka ƙaddamar a dajin Sambisa da ke jihar Borno. Wannan aikin, a cewar sanarwar da shalkwatar sojojin ta fitar ta ce ya gudana ne a ranar 11 ga watan Mayu, 2025, a yankin Ladin Buttu, "wurin da aka san shi da zama mafakar ’yan ta’adda" kuma rundunar sojin ta bayyana nasarar a matsayin muhimmin ci gaba a yaƙin da ake yi da ƙungiyar Boko Haram a Arewa maso gabashin ƙasar. Hakan na zuwa ne bayan sabbin hare-haren da mayaƙan Boko Haram suka ƙaddamar kan wurare daban-daban a jihar Borno, inda matsalar rikicin Boko Haram ta fi ƙamari. A sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X, mataimakin daraktan hulda da jama’a na Sojojin, Kyaftin Reuben Kovangiya...
Za mu koma aikin haƙo ɗanyen mai a arewacin Najeriya – NNPCL

Za mu koma aikin haƙo ɗanyen mai a arewacin Najeriya – NNPCL

Duk Labarai
Shekara biyu bayan ƙaddamar da aikin haƙo ɗanyen man fetur a iyakar jihohin Bauchi da Gombe - wanda tun daga wancan lokaci ba a ci gaba da aikin ba - a yanzu sabon shugaban kamfanin man fetur na Najeriya Bayo Ojulari ya fada wa BBC cewa za a koma kan aikin. Aikin da aka ƙaddamar a gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da ta gabata, ya sanya al’ummar arewacin ƙasar sun fara kyakkyawar fatan cewa yankin zai bi sahun wasu yankunan ƙasar da ke samar da man fetur wanda tattalin arzikin ƙasar ya dogara a kai. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan Najeriya suke cigaba da kokawa kan tsadar rayuwa, wadda ke da alaƙa tashin farashin man fetur a sanadiyar cire tallafin da gwamnati ke bayarwa a bangaren. Tun a jawabin Shugaban Najeriya Bola Tinubu na farko bayan shan rantsuwar kama mulki ne ...