Rahotanni sun bayyana cewa, Kiristoci 104 ne suka karbi Musulunci a wani kauye na jihar Delta dake kudancin Najeriya.
Hakan na zuwane yayin da ake yada rade-radin cewa ana yiwa Kiristoci kisan Khiyashi a Kasarnan wanda har aka gayyato kasar Amurka ta kawo musu dauki.
Wata matashiya me suna Fatima ta jawo cece-kuce sosai bayan data bayar da labarin yanda ta kaya tsakaninta da wani Saurayi me tuka Toyota Corolla.
Tace tana tafiya ya tsayar da ita a titi.
Tama rasa abinda zata ce masa amma tace duk wanda yasan yana tuka Toyota Corolla kada yace zai mata magana dan ta wuce da saninsa.
https://twitter.com/big__teee/status/1988694574135668834?t=26eedVkoQOS_I_JvpIsACQ&s=19
Bidiyon yanda hukumar kula da Abuja ta dauke motar rushe gini data kai filin sojoji ya watsu sosai a kafafen sada zumunta.
Motar dai itace Wike ya kai da niyyar rushe ginin da aka fara a filin sojojin amma sojan ruwa, AM. Yerima ya hanashi.
An ga mutane suna shewa suna tafi da murna yayin da ake dauke motar rushe ginin.
https://twitter.com/emmaikumeh/status/1988984236507009321?t=MJs6t33MO48jWoWQSHJ8VA&s=19
Wani dan Arewa dake zaune a kudancin Najeriya ya tsinci wayar iPhone 13 promax ya mayarwa da mai ita.
Mutumin sunansa Sulaiman, ya bi sahun matar ya mayar mata da wayarta.
Matar tace ta hau Keke Napep ne ta yadda wayar tata inda bayan da mutumin ya mayar mata da wayar ta rika rungumarsa tana murna tana gode masa.
kalli Bidiyon anan
https://www.youtube.com/watch?v=ZyXOP65wsjY?si=SsQKrf1Z93sR5exq
Hukumar kula da harkokin man fetur a Najeriya ta ce ta dakatar da shirin fara karɓar harajin kashi 15 cikin 100 kan albarkatun man fetur ɗin da ake shigarwa ƙasar daga ƙasashen waje.
Mai magana da yawun hukumar Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), George Ene-Ita, ya faɗa cikin wata sanarwa a ranar Alhamis cewa ya kamata 'yan Najeriya su daina fargaba.
A ranar 29 ga watan Oktoba ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da saka harajin kan man fetur da dizel, wanda zai ƙara farashin man da ake saukewa a defo-defo, kuma ɗaya daga cikin manufarta shi ne ƙarfafa matatun mai na cikin gida.
Gwamnatin Najeriya ta tsara fara aiki da harajin daga ranar 21 ga watan Nuwamban nan, kafin matakin da NMDPRA ta sanar.
Duk da manufar ƙarfafa matatun mai na cik...
Tauraruwar kafafen sada zumunta, Saifan Maikyau ta jawo hankalin sauran mata da cewa su daina saka hoton sojan ruwa, AM. Yerima suna cewa, suna sonsa saboda mijintane.
Mata da dama ne suka rika saka hoton sojan tun bayan Tirka-Tirkar da yayi da ministan Abuja, Nyesom Wike ya hanashi shiga fili.
Lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta.
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa, yana girmama sojoji kuma bashi da matsala dasu.
Ya bayyana hakane a yayin da ake ci gaba da takaddama akan Tirka-Tirkar data faru tsakaninsa da sojan ruwa, AM. Yerima wanda ya hanashi shiga wani fili a Abuja.
Wike yace ya je wajanne bayan samun rahoton cewa, an ciwa daya daga cikin ma'ikatansa Zarafi, yace shi kuma ba zai bari a rika ciwa ma'aikatan dake karkashinsa zarafi ba.
Yace idan an kaika wajan gadi a matsayin jami'in tsaro aka ce ka harbi mutum, idan ka kashye mutum kana tunanin doka ba zata yi aiki akanka bane?
Yace bashi da matsala da sojoji da yasan yana da matsala da sojoji akwai inda zai je ya warware matsalar.
Rahotanni na ta yawo a kafafen sada zumunta cewa, Wai tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya baiwa sojan ruwa da suka kara da Wike, A. Yerima dankareriyar motar Alfarma.
Saidai a sanarwar da ya fitar ta bakin magana da yawunsa, Paul Ibe, Atiku Abubakar yace ba gaskiya bane be baiwa AM. Yerima kyautar mota ba.
Yace labarin karyane kuma yana kira ga mutane su yi watsi dashi.
An dai rika yada cewa Atiku Abubakar ya baiwa sojan ruwan, AM. Yerima kyautar motar Toyota SUV.
Tun bayan da aka samu wata hatsaniya a ranar Talata da yamma 11 ga watan nan na Nuwamba 2025, a tsakanin ministan babban birnin Najeriya, Abuja, Nyesom Wike da jami'an sojin ƙasar saboda sojojin sun hana ministan shiga wani fili, ake ta yaɗa labarai da ra'ayoyi daban-daban a kan lamarin.
Baya ga fassara da ake yi wa lamarin ta ɓangarori daban-daban - na siyasa da mulki da kuma dokoki da ƙa'idoji na mulki, wani abu kuma da ke ɗaukan hankalin jama'a shi ne, jagoran sojojin da suka yi wannan dambarwa da ministan na Abuja da tawagarsa.
Jagoran tawagar sojojin shi ne Laftanar AM Yerima, wanda matashin ƙaramin hafsan sojin ruwa na Najeriya ne, wanda kuma ya kasance ne a wajen bisa umarnin mai gidansa tsohon shugaban rundunar sojin ruwa ta Najeriya, Vice Admiral Awwal Zubairu Gambo (mai rit...