Wednesday, January 14
Shadow
Kalli Bidiyon: Na dade da daina hawa Bidiyo ina kalaman da basu dace ba, Masu saka hotona suna rubutun da bai dace ba na barku da Allah>>Inji Habiba Dorayi

Kalli Bidiyon: Na dade da daina hawa Bidiyo ina kalaman da basu dace ba, Masu saka hotona suna rubutun da bai dace ba na barku da Allah>>Inji Habiba Dorayi

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Habiba Dorayi ta bayyana cewa tun dambarwar da aka yi a kwanakin baya har aka kama ta ta daina hawa Bidiyo tana maganganun batsa. Tace amma wasu na amfani da hotunanta a Facebook suna dora maganganun batsa. Tace su ji tsoron Allah su daina ko kuma ta barsu da Allah ya isa. https://www.tiktok.com/@habibadorayi/video/7586296430499826961?_t=ZS-92SfckjUxCT&_r=1
Kalli Bidiyon: Duk matsayinka sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya sa maka hannu zaka kai labari a ranar Qiyama>>Malam ya mayarwa da Dr. Hussain Kano Raddi

Kalli Bidiyon: Duk matsayinka sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya sa maka hannu zaka kai labari a ranar Qiyama>>Malam ya mayarwa da Dr. Hussain Kano Raddi

Duk Labarai
Malam ya mayarwa da Dr. Hussain Kano raddi kan kalaman da yayi cewa baya son Allah ya kaishi matsayin da sai ya nemi taimakon Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) kamin ya shiga Aljannah a ranar tashin qiyama. Malam yace wannan magana rashin ladabi ce. Yace kuma duk matsayinka sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya sa maka hannu kamin ka kai labari a ranar qiyama. https://www.tiktok.com/@izzalatul.bidia/video/7586796033049431352?_t=ZS-92SeWiJppTd&_r=1
Kalli Bidiyon: Yanda Ministar Al’adu da Yawon Bude Ido, Hannatu Musa Musawa ta dauki wata tsohuwa dake tafiya da kyar zuwa masallaci a motarta, ta kaita masallacin

Kalli Bidiyon: Yanda Ministar Al’adu da Yawon Bude Ido, Hannatu Musa Musawa ta dauki wata tsohuwa dake tafiya da kyar zuwa masallaci a motarta, ta kaita masallacin

Duk Labarai
Ministar al'adu da yawon Bude Ido, Hannatu Musa Musawa ta dauki hankula bayan da aka ganta ta dauki wata tsohuwa dake tafiya da kyar zuwa masallaci ta kaita masallacin. Da yawa sun jinjina mata kan irin wannan abin da ta yi. Ministar ta kai ziyara ne wajan da Tauraruwar Kannywood, Hannatu Bashir ke gina wajan sayar da abinci anan ne ta hadu da tsohuwar. https://www.tiktok.com/@hannatubashir3/video/7585998380279598344?_t=ZS-92SbWMLLG5p&_r=1
Dan Gidan Gwamnan jihar Edo ya jawo cece-kuce bayan da ya rabawa hadimansa Motoci 10

Dan Gidan Gwamnan jihar Edo ya jawo cece-kuce bayan da ya rabawa hadimansa Motoci 10

Duk Labarai
Dan gidan Gwamnan jihar Edo, Sheriff Junior Oborevwori ya jawo cece-kuce sosai bayan da ya rabawa hadimansa motoci 10. Da yawa na tambayar ina ya samu kudin da yayi wannan hidimar musamman ganin cewa, baya iya yin hakan lokacin mahaifinsa ba ya matsayin Gwamna. https://twitter.com/afrisagacity/status/2003371249377116222?t=estxyBap851Gh245DrtZJA&s=19
Rahotanni sun ce kasar Amurka tanata Tattara bayanan Sirri akan Najeriya ta hanyar amfani da jirgi marar Matuki

Rahotanni sun ce kasar Amurka tanata Tattara bayanan Sirri akan Najeriya ta hanyar amfani da jirgi marar Matuki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa tun a watan Nuwamba, kasar Amirka na ta tattara bayanan sirri akan Najeriya. Rahoton yace an gano hakanne ta hanyar amfani da na'urar dake bibiyar jiragen sama. Kafar Reuters ce ta ruwaito wannan labari. Labarin na zuwane yayin da kasar Amurka tace ba zata yi amfani da karfin soji ba a Najeriya dan taimakon Kiristoci da aka ce ana kashewa.
Kasar Ghana ta koro ‘yan Najeriya 42 da suka je cirani kasar

Kasar Ghana ta koro ‘yan Najeriya 42 da suka je cirani kasar

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Ghana na cewa, kasar ta koro 'yan Najeriya 42 da suka je chirani kasar. Kasar ta kori jimullar 'yan kasashen waje 68 daga yankin Ashanti bayan da aka samesu da aikata miyagun laifuka, irin su Qaruwanchi, da sauransu. Hukumomin kasar sun ce sun dauki wannan mataki ne dan tsaftace kasarsu da kuma kiyaye al'ummarsu daga miyagun laifukan da bakin ciranin ke yi.
Da Duminsa: Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa wajan Maulidi sun bace a kauyen Zak dake jihar Filato

Da Duminsa: Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa wajan Maulidi sun bace a kauyen Zak dake jihar Filato

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Filato na cewa, Musulmai 12 dake kan hanyar zuwa Maulidi a Karamar hukumar Wase jihar Filato sun bace. rahotanni sun wasu Tshàgyèràn Dhàjì Kiristoci ne suka yi garkuwa dasu. Garkuwar ta farune ranar 21 ga watan Disamba a daidai kauyen Zak. Wani shaida ne ya kai rahotan faruwar lamarin. Kafar Zagazola Makama tace jami'an tsaro sun je wajan inda aka fara neman wanda aka dauke din.