Monday, April 6
Shadow
Kuma Dai: Shugaban Kungiyar dalibai ya maka dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da Shugaban DSS da shugaban NTA a kotu inda yake neman a biyashi diyyar Naira Biliyan 38.3

Kuma Dai: Shugaban Kungiyar dalibai ya maka dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da Shugaban DSS da shugaban NTA a kotu inda yake neman a biyashi diyyar Naira Biliyan 38.3

Duk Labarai
Shugaban kungiyar daliban Najeriya, Comrade Atiku Abubakar Isah, ya maka dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da shugaban gidan talabijin na kasa, NTA, da shugaban hukumar tsaron farin kaya, DSS a kotu inda yake neman a biyashi diyyar Naira Biliyan 38.3. Ya kuma nemi a sakeshi daga tsaron da ake masa na tsawon kwanaki 14 wanda ya bayyana da cewa garkuwa ce aka yi dashi. Hakanan ya kuma bayyana cewa yana neman kotu ta dakatar da bata masa sunan da ake yi, inda yace kuma tsaron da akw masa an take hakkinsa na walwala kamar yanda Kudin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa kowane dan kasa damar yi. Dan haka yake neman kotun tarayya dake Abuja ta bi mai hakkinsa, ya shigar da karar ne ta hannun lauyansa, Ugwueze I. Oduegbu da R.O. Ifebhor. An dai kama Kwamared Isa ne bayan da ya zargi Dan shug...
Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya soki kasashen Larabawa saboda karrama Shugaban kasar Amurka Donald Trump yayin da akewa Falasdiynawa Kìsàn Kiyashi

Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya soki kasashen Larabawa saboda karrama Shugaban kasar Amurka Donald Trump yayin da akewa Falasdiynawa Kìsàn Kiyashi

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya soki kasashen Larabawa inda ya kirasu da munafukai saboda yanda suka tarbi shugaban kasar Amurka, Donald Trump suka bashi kudade na fitar hankali dan ya je ya zuba jari a kasarsa. Kasashen da Trump ya je sune Saudiyya, Qatar, da UAE. https://twitter.com/el_uthmaan/status/1923238869039726928?t=RVrz9PM8VPKMldyHE70bXA&s=19 Sheikh Gumi yace wannan kudade da suka baiwa Amurka, kamar sun baiwa Israela ne yace dan ba zaka raba Israela da Amurka ba. Yace malaman kuma da suka yi shiru to suna da raunin Imanine.
An kama dan wasan Real Madrid da yiwa karamar yarinya fyàdè

An kama dan wasan Real Madrid da yiwa karamar yarinya fyàdè

Duk Labarai
'Yan wasan Real Madrid 4 ciki hadda Raul Asencio zasu iya fuskantar hukunci bayan yada Bidiyon badala da wasu mata biyu ciki hadda wata karamar yarinya wadda shekarunta basu kai 18 ba. Alkalin dake shari'ar yace ya kammala nazarin Bidiyon wanda aka dauka wani wajan shakatawa. Alkalin yace matan dake cikin Bidiyon daya shekarunta 18 dayar kuma shekarunta 16. Alkalin yace laifukan da ake zargin 'yan wasan dasu sune yada Bidiyon da aka dauka a sirce ba tare da izinin wadandake cikin Bidiyon ba da kuma amfani da karamar yarinya
Gwamnatin jihar Bauchi ta tallafawa tubabbun mata 100 Karuwai da koyon sana’a

Gwamnatin jihar Bauchi ta tallafawa tubabbun mata 100 Karuwai da koyon sana’a

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Bauchi ta tallafawa tubabbun mata karuwai da masu shaye-shaye da suka daina da kayan sana'a dan dogaro da kai. An tattaro matanne daga karamar hukumar Misau ta jihar ta Bauchi wanda ke karuwanci da shaye-shaye inda aka tallafa musu a karkashin tsarin Better Life Restoration Initiative (BERI). Daya daga cikin matan da suka amfana da wannan lamari ta bayyana cewa ta samu canjin rayuwa a yanzu an bata sana'a amma tace matsalar daya ce shine har yanzu ana hantararsu.
YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Ya Ƙaddamar Da Sabbin Jiragen Yaƙi Masu Saukar Angulu Samfurin Agusta A-109Power Attack

YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Ya Ƙaddamar Da Sabbin Jiragen Yaƙi Masu Saukar Angulu Samfurin Agusta A-109Power Attack

Duk Labarai
Shugaba Tinubu Ya Ƙaddamar Da Sabbin Jiragen Yaƙi Masu Saukar Angulu Samfurin Agusta A-109Power Attack A wani ɓangare na kokarin sabunta tsarin tsaron ƙasa. Shugaba Tinubu ya wakilta mataimakinsa Kashim Shettima wajen kaddamar da Sabbin jiragen yaƙin Shettima ya jaddada kudirin gwamnatin Najeriya na shiga dumu-dumu hannun cikin harkar inganta sabbin fasahohin aiyukan tsaron ƙasa domin wadata sojojin Najeriya da abubuwan da suka dace don tunkarar kalubalen tsaro. Gwamnatin ta kuma tabbatar wa da hukumar sojojin saman Najeriya ta NAF da cewa za ta sami ƙarin jiragen yaƙi sama 49 a cikin shekaru biyu masu zuwa. Shugaban ya kuma bukaci sojojin saman da su kiyaye ɗa'a da bin ƙa'idojin aiki don cin gajiyar manufofin aiki
Mummunan hàrì yayi sanadiyyar salwantar rayuka 10 a jihar Filato

Mummunan hàrì yayi sanadiyyar salwantar rayuka 10 a jihar Filato

Duk Labarai
Aƙalla mutum 10 ne aka kashe tare da sace shanu a wani sabon rikici da ya ɓarke a yankin ƙaramar hukumar Riyom a jihar Plateau. Sabon rikicin ya samo asali ne daga lalata amfanin gona da sace shanu da kashe wasu dabbobin, kamar yadda Gidan Talbijin na Channels a ƙasar ya ruwaito. Cikin wata sanarwa da rundunar soji ta 'Operation Safe Haven' ta fitar ta ce rikicin ya fara ne tun a ranar Litinin 12 ga watan Mayun da muke ciki, a lokacin da aka zargi wasu fusatattun matasa da kashe wasu shanu da suka yi zargin sun shiga gonakinsu a ƙauyen Dayan da ke ƙaramar hukumar ta Riyom. A ranar 13 ga watan ne kuma aka zargi wasu makiyaya da kai hari ƙauyen Danchindo domin ramuwar gayya, tare da kashe mutum huɗu kafin su tsare bayan zuwan jami'an tsaro. Haka kuma a ranar 14 aka zargi wasu mah...
Sai Talaka ya Dara: Na sha Alwashin karya farashin shinkafa warwas>>Inji BUA

Sai Talaka ya Dara: Na sha Alwashin karya farashin shinkafa warwas>>Inji BUA

Duk Labarai
Shugaban rukunin kamfanonin kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta sake rage farashin shinkafa da sauran kayan abinci, wanda ya ce tun shekarar da ta gabata yake ta sauka. Abdul Samad Rabiu ya bayyana haka ne ranar Alhamis jim kaɗan bayan ganawarsa ta Tinubu a fadar shugaban ƙasar. Shugaban na BUA ya yaba wa Tinubu kan bayara da damar shigo da wasu kayan abinci da ya yi, yana mai bayyana matakin da 'kyakkyawa'' da ya ce ya taimaka wajen karyewar farashin kayan abinci a ƙasar. A watan Yulin 2024 ne gwamnatin Shugaba Tinubu ta bayayna dakatar da karɓar kudin fito na shigo da kayan abinci a wani mataki na magance hauwarar farashin kayayyaki. BUA ya zargi masu sayen kayyaki domin ɓoyewa da haddasa tashin farashin. Ya ce da zarar lokacin girbe amfanin gona ya yi, sai wasu ...
Ba ma fatan Najeriya ta zama ƙasa mai bin tafarkin jam’iyya ɗaya – APC

Ba ma fatan Najeriya ta zama ƙasa mai bin tafarkin jam’iyya ɗaya – APC

Duk Labarai
Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar APC, Felix Morka, ya bayyana cewa duk da ƙaruwar mutane da ke sauya sheka zuwa jam’iyyar, jam’iyyar mai mulki ba ta da niyyar mayar da Najeriya ƙasa mai jam'iyya ɗaya tak. Ya bayyana cewa a lokacin da Jam’iyyar PDP, ke mulki, ta rike fiye da jihohi 28 ba ba a zarge ta da ƙoƙarin mayar da ƙasar ta zama ƙasa mai jam'iyya ɗaya ba. Morka ya ce babu wani laifi ga mambobin jam'iyyun PDP da LP da ke sauya sheka zuwa APC idan suna son su haɗa kai da tsarin jam’iyyar mai mulki. Ya ce, “Da yawa daga cikin waɗannan mutane na shigowa a cewarsu don zama a ɓangaren da ke kan tsari. “A ƙasar mu, duka a cikin ƙundin tsari dokar zaɓe, da kuma sauran dokoki da dama, akwai tsarin da ya tabbatar da cewa Najeriya ƙasa ce mai jam’iyyun siyasa da dama kuma al’umma ...
Tinubu zai halarci bikin rantsar da sabon fafaroma

Tinubu zai halarci bikin rantsar da sabon fafaroma

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai halarci bikin rantsar da sabon fafaroma, Leo XIV da za a gudanar a birnin Rome na asar Italiya. Cikin wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar, ta ce Tinubu zai tafi Rome a ranar Asabar domin halartar bikin, bisa gayyatar da sabon fafarman ya aike masa. Sanarwar ta ce Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariar Katolika na Najeriya domin shaida bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267. Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ''ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami'ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980''.
Rashin tsaro: Tinubu na ganawa da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasa

Rashin tsaro: Tinubu na ganawa da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasa

Duk Labarai
A halin yanzu shugaba Bola Ahmed Tinubu ya na wata ganawar sirri da shugabannin hukumomin tsaro da kuma babban sufeton ƴansanda na kasa (IGP) a fadar shugaban kasa da ke Abuja. DAILY TRUST ta rawaito cewa wadanda su ka halarci ganawar sun hada da babban hafsan tsaron kasa, Janar Christopher Musa; Babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede; Hafsan Hafsoshin Sojan Sama, Air Marshal Hassan Abubakar; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla; da Sufeto Janar na ƴansanda, Kayode Egbetokun. Ko da ya ke ba a fayyace cikakken bayanin taron ba har zuwa lokacin da Trust ta buga labarin, amma tattaunawar ba za ta rasa nasaba da sabbin hare-haren ƴan ta'adda a wasu sassan kasar ba.