Monday, December 15
Shadow
Babu lungu da sakon da ba’a shaida salon Mulkina ba a Najeriya>>Shugaba Tinubu

Babu lungu da sakon da ba’a shaida salon Mulkina ba a Najeriya>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, babu lungu da sako na kasarnan da ba'a shaida salon mulkinsa ba a Najeriya. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin me bashi shawara akan harkar sadarwa, Daniel Bwala a yayin da ake hira dashi a gidan talabijin na TVC. Bwala yace shugaba Tinubu a yayin da yazo kan mulki akwai jihohi kusan 19 dake fama da matsalar karancin kudi wanda cire tallafin man fetur da Tinubu yayi gwamnati ta samu karin kudin shiga sosai yasa jihohin suka farfado daga hanyar talaucewa da suka kama. Bwala ya kara da cewa, an samu ci gaba sosai kuma kowane lungu da sako na kasarnan sun shaida hakan. Yayi kira ga gwamnonin dasu tabbatar da sun bayar da ci gaban da ake bukata a jihohinsu.
Khalifa Aminu, fasihin yaron nan dan jihar Kano mai ƙere-ƙere, ya ƙirƙiri wata sabuwar na’ura mai nuna yanayin jini da jikin ɗan adam

Khalifa Aminu, fasihin yaron nan dan jihar Kano mai ƙere-ƙere, ya ƙirƙiri wata sabuwar na’ura mai nuna yanayin jini da jikin ɗan adam

Duk Labarai
. Ga bayanin na'urar nan da ya wallafa a shafin sa na Facebook. " Wannan shine sabon 'project' dina mai ban mamaki da ban al ajabi wato 'Scan blood & temperature device'. "Wato na'urar mai gano bugun jini da yanayin jiki. Wannan na'urar za ta iya temaka wa mutane da dama wajan kare lafiyar jikinsu. "Ita dai wannan na'urar ana saka ta a hannu ne. Bayan ka saka ta a hannu to duk inda ka shiga idan zafi yai yawa a wajen ko sanyi ko yanayin iskar da ka ke shaƙa to za tayi scaning din jikin ka ta ga yanayin 'temperature' din da jikin ka ya ke bukata idan wannan yanayin iskar ko zafi ko sanyi su kai yawa nan take za ta sanar da kai kabar wajen idan ba haka ba zaka iya cutuwa. "Sannan za ka iya scan din jinin jikin ka don ka ga lafiyar ka kalau ko ba ka da lafiya. " Wann...
An gano ƙanƙara mai shekara fiye da miliyan ɗaya a duniya

An gano ƙanƙara mai shekara fiye da miliyan ɗaya a duniya

Duk Labarai
Masana kimiyya a nahiyar Turai sun gano ƙanƙarar da watakila ake ganin ita ce mafi daɗewa a duniya a yankin Antarctica. Tawagar masu binciken ta haƙo silindar ƙanƙarar mai tsawon kusan kilomita uku wanda ke ɗauke da tsohon kumfa da kuma ɓurɓushi da aka daina ganin irinsa tun fiye da shekara miliyan guda. Masanan na fatan cewa yin nazarin tarihin yanayin zafi da matakan iskar gas zai taimaka musu wajen hasashen sauyin yanayi a nan gaba. Tuni dai masu binciken suka yayyanka ginshiƙin ƙanƙarar zuwa sassa masu tsayin mita ɗaiɗai domin faɗaɗa bincike a cibiyoyin bincike a faɗin nahiyar Turai.
Tinubu ya yi alhinin sojojin Najeriya da suka mùtù a harin Damboa

Tinubu ya yi alhinin sojojin Najeriya da suka mùtù a harin Damboa

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yi alhinin rasuwar dakarun ƙasar, da aka kashe a harin da mayaƙan Boko Haram ta kai wani sansanin soji da ke ƙauyen Sabon Gida, cikin ƙaramar hukumar Damboa a jihar Borno. Cikin wata sanarwa da fadar gwamnatin ƙasar ta fitar, ta ce Tinubu ya jajanta wa rundunar sojin ƙasar sakamakon mutuwar dakarunta shida a harin. Haka kuma shugaban ƙasar, ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike domin gano abin da ya haddasa harin, domin ɗaukar matakan hana faruwar makamancinsa a nan gaba''. A ranar Asabar ne mayaƙan ISWAP suka ƙaddamar da hari da asuba kan sansanin sojin inda suka yi arangama da sojoji, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin ƙasar shida da mayaƙa fiye da 30. Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa sojojin ƙasar bisa jajirewar da suka yi, har ta k...
Za a ƙara kuɗin kiran waya a Najeriya – Gwamnatin Najeriya

Za a ƙara kuɗin kiran waya a Najeriya – Gwamnatin Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da shirin ƙara kuɗin kiran waya da na data, nan ba da jimawa ba. Ministan sadarwar ƙasar, Bosun Tijani ne ya bayyana haka a lokacin ganawa da masu ruwa da tsaki a Abuja. Ya ce hukumar sadarwa ta ƙasar, NCC ce za ta tsara yadda ƙarin zai kasance. Tijani ya ƙara da cewa, “Kafin mu zo da wannan shawara, sai da muka yi la'akari da abubuwa masu yawa na yadda hakan zai taimaka wajen gina ƙasarmu''. “Wasu daga cikin abubuwan sun haɗa da tabbatar da inganta hanyoyin sadarwarmu da inganta kamfanoninmu na cikin gida da tabbatar da ɗorewar kamfanonin kansu''. ''Haka ma kamar yadda muke ganin hauhawar farashin kayayyaki a duniya, su ma kamfannonin sadarwar na fuskantar wannan matsala, don haka ba za mu bari su durƙushe ba, dole mu yi wani abu don tabbatar ...
Ƴan sintiri sun ceto mutum 63 a hannun masu garkuwa a Sokoto

Ƴan sintiri sun ceto mutum 63 a hannun masu garkuwa a Sokoto

Duk Labarai
Tawagar ƴan sintiri a jihar Sokoto ta ce ta kuɓutar da mutum 63 daga hannun masu garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa, a jihar mai fama da matsalar ayyukan ƴan bindiga. Wata sanarwa da ta samu sa hannun Garba Mohammed, mai magana da yawun mataimakin gwamnan jihar ta ce tawagar ta ƙunshi jami'an ƴansanda da jami'an tsaro ƙarƙashin gwamnatin jihar Sokoto. Bayanin ya bayyana cewa an kuɓutar da mutanen ne a tsawon kwana huɗu, daga ranar Lahadin da ta gabata. Sokoto na daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya masu fama da matsalar ƴan bindiga masu satar mutane domin neman kuɗin fansa. Haka nan a baya-bayan nan an samu ɓullar wata ƙungiyar ƴan bindiga da ake kira Lakurawa. Rundunar sojin Najeriya ta ce ta tsananta ayyukan yaƙar ƴan bindiga tun bayan ɓullar ƙungiyar ta...
NAPTIP ta kuɓutar da mutum 285 da aka yi safararsu zuwa Kano a 2024

NAPTIP ta kuɓutar da mutum 285 da aka yi safararsu zuwa Kano a 2024

Duk Labarai
Hukumar yaƙi da safarar mutanen da Najeriya, NAPTIP, reshen jihar Kano ta ce ta kuɓutar da wasu mutum 285 da aka yi yunkurin safararsu tare da kama masu safarar 22 a shekarar 2024. Kwamandan hukumar a reshen jihar, Abdullahi Babale ne ya bayyana haka cikin wata hira da kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN a Kano. Babale ya ce daga cikin mutum 285 da aka kuɓutar, 78 maza ne, yayin da 97 daga ciki mata ne, da ƙananan yara 110. Yayin da babban jami'in hukumar a jihar Kano ya ce sun kama mutum 22 bisa zargin hannu a laifin ciki har da maza takwas da mata 14. Abdullahi Babale ya ce laifukan da ake zarginsu sun haɗa da cin zarafin ƙananan yara da tilasta musu aikin ƙarfi, da cin zarafi ta hanyar lalata da sauran laifuka ƙarƙashin dokokin cin zarafin ɗan'adam.
Gwamnatin Bauchi ta ware Naira miliyan 400 don sayen kwamfuta guda shida ga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar

Gwamnatin Bauchi ta ware Naira miliyan 400 don sayen kwamfuta guda shida ga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar

Duk Labarai
Gwamnatin Jihar Bauchi ta ware Naira miliyan 400 a cikin kasafin kudin shekarar 2025 don sayen kwamfuta guda shida domin ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar. Jaridar The Guardian ta rawaito cewa, haka kuma, gwamnatin jihar ta ware Naira biliyan daya don “sayen fili domin gina ofisoshi da gine-gine.” Za ta kuma kashe Naira miliyan 170 don sayen janareta domin samar da wutar lantarki a ofishin SSG. Mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Ibrahim Musa, ya soki wannan kasafi, yana mai bayyana shi a matsayin rashin fifikon abubuwan da suka dace a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke fama da wahalhalu sakamakon manufofin tattalin arzikin gwamnati. Musa ya bukaci Gwamnatin Jihar Bauchi da ta kauce wa yin hakan tare da mayar da hankali kan ayyukan da za su kawo ci gaba a rayuwar al’ummar jiha...