Tuesday, July 21
Shadow

Amfanin ganyen ayaba

Duk Labarai
Akwai amfani da yawa da ake yi da ganyen ayaba da suka hada da dafa abinci, gasawa, dama zuba abinci a ciki a ci da kuma yin kwalliya dashi. Ana amfani da ganyen Ayaba a matsayin kwano a zuba abinci a ciki wanda da zarar an kammala cin abincin sai a yadda. Yawancin an fi yin hakan a kasashen Asia. Ana kuma yin amfani dashi wajan gasawa ko dafa abinci, Yarbawa kan yi amfani dashi wajan nada Alale a ciki a dafa. Sannan ana nade wasu abubuwa a ciki a gasa. Hakanan akan yi amfani da ganyen ayaba wajan magance kaikayin fata da kuma ciwo ko bacin ciki.

Ganyen mangoro da amfaninsa

Duk Labarai
Ganyen mangoro na da amfani sosai a jikin dam adam. A wannan rubutu, zamu duba amfanin ganyen Mangoro ga lafiyar dan Adam. A dunkule, Ganyen Mangoro na maganin ciwon sugar, yana hana fata da jiki saurik tsufa, yana maganin Kumburin jiki, ana kuma amfani dashi wajan magance kuna da aka samu dalilin wuta, da kuma idan abinci baya sarrafuwa a jikin da adam. Ganyen Mangoro na kuma taimakawa tsawon gashi kuma ana zubashi a ruwan wanka ko a hada shayi dashi saboda yana kara nutsuwa da kawar da damuwa. Ganyen Mangoro na maganin ciwon gabobi na tsufa. Ganyen Mangoro na maganin ciwon Ulcer da Gudawa da kukan ciki da sauransu. Ganyen Mangoro na maganin cutar Asama. Ganyen Mangoro na taimakawa wajan hana furfura da wuri da kuma kara tsawon gashi, idan mutum ya kone da wuta, gany...

Gajerun kalaman yabon budurwa

Kalaman Soyayya
Ga gajerun Kalaman Yabo ga Budurwa kamar haka: Kin hadu. Kin yi kyau. Murmushinki na burgeni. Kayannan sun zauna a jikinki daidai. Kece fitila ta. Kece Madubina. Duk randa na kalleki gaba dayan ranar farin ciki nake kasancewa dashi. Zan zo daukar darasin Murmushi saboda ban taba ganin irin murmushinki ba. Allah ya miki ni'imomi da yawa, amma wacce ta fi burgeni shine iya kalamanki. Kin kasance maganin damuwata. Duk sanda raina ya baci, muryarki na kwaranye damuwata. Rayuwarki abar koyi ce ga mata da yawa dan kina da dabi'u masu kyau da suka dace da addini. Kece Filitar Rushina. Kece me sani dariya. Kece Ice cream dina. Inna ganki da safe ba sai na karya ba. Fuskarki ko ba mai tana sheki. Idan ta nine ba sai kin yi kwalliya ba dan a haka...
Ya’yan Aliko Dangote

Ya’yan Aliko Dangote

Duk Labarai
'Ya'yan Aliko Dangote wanda ya haifa 3 ne kuma dukansu mata ne amma akwai guda daya na miji wanda dan riko ne. 'Ya 'yan Dangote mata wadanda ya haifa 3 sune: Fatima Dangote. Mariya Dangote. Halima Dangote. Dan da yake riko shine:Abdulrahman Fasasi wanda ba shine ya haifeshi ba. Duka 'ya'yan na Dangote na taimakawa sosai wajan gudanar da kasuwancinsa inda sukan jagoranci wasu fannoni na kasuwancin. Matan Dangote nawane Dangote ya taba aure sau 2 saidai duka matan ya rabu dasu Matar Dangote ta farko sunanta, Zainab kuma da ita ya haifi Halima da Mariya, saidai daga baya ya saketa. Hakanan Dangote ya sake auren wata matar me suna Mariya Muhammad Rufai wadda da itace ya haifi Fatima, itama kuma ya saketa. A yanzu dai, daidai lokacin wannan rubutu, Dangote ba...

Da gaske Ronaldo ya musulunta?

Duk Labarai
Masoyan dan kwallon kafa, Cristiano Ronaldo musamman Musulmai sai doki suke dan sanin cewa wai da gaske ya musulunta? Hakan bai rasa nasaba da kasancewarsa yana buga kwallo a kasar Saudiyya wadda kasa ce me tsarki ga Musulunci. Musuluntar Cristiano Ronaldo zata dauki hankula sosai a tsakanin masoyansa da wadanda ma ba masoyansa ba. A bayanan da muke dasu a yayin wannan rubutu, babu wata sahihiyar kafa data tabbatar da cewa, Cristiano Ronaldo ya musulunta. Saidai muna fatan Allah yasa nan gaba ya musulunta.

Ta yaya ake tantance labari

Duk Labarai
Ana Tantance labarine ta hanyar bincike dan gane sahihancin kafar data wallafashi. Ma'ana, kafar data wallafa labarin sahihiya ce, ta saba wallafa labaran gaskiya, sannan sabuwa ce ko tsohuwar kafar yada labarai wadda mutane da yawa suka sani? Sannan ana gane sahihancin labari idan ya zamana kafafen yada labarai da yawa manya da kanana duk sun wallafashi. Ana kuma gane sahihancin labari idan ya zamana an yi hira da wadanda abin ya faru dasu ko ya faru a gaban idanunsu watau shaidu. Ana kuma gane sahihancin labari idan ya zama cewa, an ga Bidiyon faruwar lamarin daga farko zuwa karshe.
Kalli Bidiyo Da Duminsa: A karshe dai, Tankokin Dakon Man fetur na Dangote guda 4000 sun iso Najeriya

Kalli Bidiyo Da Duminsa: A karshe dai, Tankokin Dakon Man fetur na Dangote guda 4000 sun iso Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni daga Legas na cewa, Tankokin dakon man fetur na Attajirin Najeriya, Aliko Dangote sun iso Najeriya. An ga Bidiyon yanda ake sauke tankokin daga jirgin ruwa inda tuni aka fara hadasu. Matatar man fetur ta Dangote ta bayyana cewa, nan da ranar 15 ga watan Augusta zata fara jigilar man fetur dinta zuwa sassa daban-daban na Najeriya da sabbin tankokin man. https://twitter.com/thecableng/status/1934887582204084562?t=DQe2Yp2SBeo2bAOBA04pYw&s=19 Saidai kungiyar direbobin tankar man Najeriya sun koka da cewa, hakan zai talautasu
Kalli Bidiyo: Soja me mukamin Kyaftin yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa mahara ke musu wayau suna galaba akansu

Kalli Bidiyo: Soja me mukamin Kyaftin yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa mahara ke musu wayau suna galaba akansu

Duk Labarai
Wani soja me mukamin kyaftin yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa 'yan Bindiga ke nasara akansu. Sojan ya bayyana cewa, Ana kama 'yan Bindigar da suka mika kansu ace an canja musu hali sai a daukesu aikin soja. Yace wannan yana sa su rika samun horaswa da sirrin sojoji wanda ke taimakawa wajan yin nasara akansu. Kalli Bidiyon sa: Kotu ta bayar da belin Tsohon Gwamnan CBN, Emefiele akan Naira Biliyan 2
Kotu ta bayar da belin Tsohon Gwamnan CBN, Emefiele akan Naira Biliyan 2

Kotu ta bayar da belin Tsohon Gwamnan CBN, Emefiele akan Naira Biliyan 2

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Babbar kotun tarayya dake Maitama Abuja ta sanar da bayar da Belin Tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele akan Naira Biliyan 2. Ranar Litinin ne kotun ta bayar da belin Emefiele bayan da aka gurfanar dashi bisa zarge-zargen cin hanci da rashawa guda 8 ciki hadda gina rukunin gidaje 753 a Abuja. An kuma zargeshi da amfani da wasu mutane 'yan uwa da abokai wajan satar kudaden Gwamnati.
Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Duk Labarai
Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur ta OPEC ta ce duk da raguwar fitar da mai da aka samu a Najeriya, har yanzu ƙasar ce ta fi kowace ƙasa yawa fitar da mai a Afirka. A cikin rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin, ƙungiyar ta OPEC ta ce fitar da ɗanyen mai daga Najeriya ya ragu zuwa ganga miliyan 1.45 a kullum a watan Mayu — daga ganga miliyan 1.48 da aka samu a watan da ya gabata. Rahoton ya bayyana cewa duk da wannan raguwar, Najeriya ta ci gaba da zama ƙasa kan gaba a yawan fitar da danyen mai a nahiyar Afirka, inda ta zarce ƙasashen Libya da Aljeriya da Kongo. OPEC ta ce ta samo wannan alƙaluma ne daga bayanan da ƙasashe suka bayar kai tsaye. OPEC ta ƙara da cewa alƙaluman da aka samu ya nuna cewa Najeriya ta fitar da ganga miliyan 1.54 a kullum a watan May...