Monday, April 6
Shadow
Dole Sabon fafaroman da za’a zaba kada ya yi irin abinda marigayi Fafaroma Francis yayi na goyon bayan ‘yan Luwadi da Madigo, Baibul ya koya aure tsakanin namiji da mace ne kawai>>Inji Wani babban Limamin Kirista

Dole Sabon fafaroman da za’a zaba kada ya yi irin abinda marigayi Fafaroma Francis yayi na goyon bayan ‘yan Luwadi da Madigo, Baibul ya koya aure tsakanin namiji da mace ne kawai>>Inji Wani babban Limamin Kirista

Duk Labarai
Wani Babban maamin Kirista daga kasar Jamus, Gerhard Ludwig Müller yayi gargadin cewa sabon fafaroman da za'a zaba kada ya zama yana goyon bayan 'yan Luwadi da Madigo. Ya bayyana cewa duk matsin lambar da za'a masa kada ya goyi bayan wannan kazanta. Yace Baibul ya koya musu aure tsakanin mace da namiji ne kawai inda ya yi Allah wadai da masu neman halasta auren jinsi. Daya daga cikin abinda marigayi Fafaroma Francis yayi suna dashi shine neman baiwa 'yan Luwadi da madigo kariya.
Kalli Bidiyon yanda abinda ya faru a Edo ya so ya sake Faruwa ga wasu ‘yan Arewa da suka tafi cirani a jihar Oyo saidai su da aka tsayar da motar tasu sun tsere

Kalli Bidiyon yanda abinda ya faru a Edo ya so ya sake Faruwa ga wasu ‘yan Arewa da suka tafi cirani a jihar Oyo saidai su da aka tsayar da motar tasu sun tsere

Duk Labarai
Wasu 'yan Arewa da aka tare a jihar Oyo yayin da suka je wucewa ta cikin jihar sun auna arziki inda duka suka tsere. A baya irin wannan ta taba faruwa a jihar Edo inda aka dake wasu mafarauta wanda aka zarga da cewa masu garkuwa da mutanene har sai da suka daina motsi sannan aka cinna musu wuta. Saidai a wannan Karin basu tsaya ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1916569234085228586?t=Gi7A32-KGIxup14WqmVJZg&s=19 An ji mutanen dake magana a cikin Bidiyon suna kiran mutanen da 'yan Bòkò Hàràm duk da yake cewa babu wata hujja data tabbatar da hakan.
An yanke wa limamin masallaci shekaru 5 a gidan yari sakamakon kàshè alade

An yanke wa limamin masallaci shekaru 5 a gidan yari sakamakon kàshè alade

Duk Labarai
Wata kotu a Rwanda ta ɗaure wani malamin addinin Islama har na tsawon shekara biyar a kurkuku sabo da ya kashe wani alade a harabar wani masallaci. Wasu shaidu uku sun shaida wa kotun cewa sun ga limamin mai suna Sadate Musengimana yana dukan aladen da wani katako matakin da ya kashe shi nan take. Sai dai lauyansa ya shaida wa kotun cewa ba da gangar ya kashe aladen ba, yana cewa ya yi kokarin koran shi daga harabar wani masallaci da ke gundumar Kayonzo a gabashin kasar ne cikin watan Fabrairu. "Da yaji yara na cewa wani alade ya shiga masallacin, sai ya fito da wata sanda domin ya kore shi. Ya daki aladen kuma ya mutu, amma bai yi niyyar kashe shi ba," kamar yadda lauyansa Yusuf Nsengiyumva ya shaida wa BBC. Lauyan ya ce ya daukaka kara kan wannan hukuncin "mai tsanani". Tu...
Ji Niqaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki

Ji Niqaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki

Duk Labarai
NiQaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki. Wanda Aka daura mana aure Dashi muna son junan mu, tun kafin bikin mu yake cewa Shi bayason ina sanya NiQaf, nikuma na fada masa irin Tarbiyyar Gidan mu kenan,baban mu baya barin kowa ta fita sai da NiQaf, Bai tashi fara nuna ɓacin Ransa akan Niqaf din sosai ba sai Ranar da yace in shirya muje shopping, aiko na dakko NiQaf shi kuma yace bazan saba, ni kuma nace sai dai in fasa fitar, daga karshe yace in zaba ko Umurnin sa ko in koma gida, bance masa komai ba dai,karshe yace ya sakeni saki Daya.
Kotu ta yi watsi da buƙatar Emefiele kan dawo masa da gidajen da EFCC ta ƙwace

Kotu ta yi watsi da buƙatar Emefiele kan dawo masa da gidajen da EFCC ta ƙwace

Duk Labarai
Wata babbar kotun tarayya a Najeriya ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele, ta neman a dawo masa da rukunin gidajen da gwamnati ta ƙwace. A ranar 2 ga watan Disamba ne hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta samu amincewar kotu domin ƙwace unguwa guda mallakar Mista Emefiele da ke Abuja babban birnin ƙasar. Unguwar da ke yankin Lokogoma ta ƙunshi gidaje 753. Tsohon gwamnan ya nemi kotun ta ƙara masa lokaci domin gabatar da buƙatar neman jingine umarnin da ta bayar na ƙwace rukunin gidajen a watan Disamban 2024. Ya yi iƙirarin cewa bai san lokacin da kotun ta yanke hukuncin ƙwace gidajen ba, sannan ya zargi EFCC da wallafa sanarwar neman mamallakin gidajen a wani "ɓoyayyen sashe na shafin jarida ta yadda zai yi wahala ya iya r...
Tashin bàm ya kàshè mutum 26 a jihar Borno

Tashin bàm ya kàshè mutum 26 a jihar Borno

Duk Labarai
Rahotanni daga arewa maso gabashin Najeriya na cewa aƙalla mutum 26 ne suka rasu ranar Litinin sakamakon tashin wani bam da motar da suke ciki ta taka a kan hanyar da ke tsakanin garin Rann zuwa Gmaboru Ngala. Kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito cewa mutanen da abin ya rutsa da su sun haɗa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida. Bam ɗin da ake zaton ƙungiyar Bòkò Haram ce ta dasa binne shi, ya kuma jikkata aƙalla mutum da dama waɗanda suke asibiti domin samun kulawa. Duk da cewa al'ummar yankin sun ɗora laifin kan ƙungiyar Bòkò Haram amma har kawo yanzu hukumomin tsaro ba su ce uffan ba.
Na kusa da Shugaba Tinubu kakkangeshi suke, basa bari a je kusa dashi ballantana a gaya masa halin da mutane ke ciki, watanni na 18 ina aiki a fadar shugaban kasa amma sau 3 muka taba haduwa da shugaban kasa shima a masallaci ne>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa da ya ajiye aikinsa, Hakeem Baba Ahmad

Na kusa da Shugaba Tinubu kakkangeshi suke, basa bari a je kusa dashi ballantana a gaya masa halin da mutane ke ciki, watanni na 18 ina aiki a fadar shugaban kasa amma sau 3 muka taba haduwa da shugaban kasa shima a masallaci ne>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa da ya ajiye aikinsa, Hakeem Baba Ahmad

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa da ya ajiye aikinsa, Hakeem Baba Ahmad ya bayyana daya daga cikin matsalolin da ya fuskanta a fadar shugaban kasar. Yace babbar matsala da suka fuskanta itace basa samun ganin Shugaban kasa a matsayinsu na wanda suke masa aiki kuma suna cikin fadar. Yace shugaban kasar baya samun bayanai na gaskiya akan halin da talakawa ke ciki. Yace a watanni 18 da yayi a fadar shugaban kasar, sau 3 kacal ya taba haduwa da shugaban kasar shima kuma a masallaci ne.