Magoya Bayan Sarki Sanusi II Sun Yi Wa Gwamna Abba Kyakkyawar Tarya A Hanyarsa Ta Dawowa Daga Filin Jirgi A Safiyar Yau Domin Nuna Farin Cikinsu Da Sake Nadin Sabon Sarkin Kanò.
Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa, me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya goyi bayan zalunci a jihar Kaduna.
Sanata Sani ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumuntar Twitter.
Sani yace Sarki Muhammad Sanusi II yana yakar zalunci a jihar Kano amma kuma a baya ya goyi bayan zaluncin a jihar Kaduna.
Sarki Sanusi dai abokine a wajan Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kuma a lokacin da aka cireshi daga mukamin sarkin Kano, ya koma Kaduna inda El-Rufai ya bashi waje ya bude fada sannan kuma ya bashi mukami a jami’ar jihar Kaduna.
Biyo bayan dambarwar data sarkake masarautar Kano, Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Dahiru Bauchi ya fitar da sanarwa.
Sheikh Dahiru Bauchi ta hannun gidauniyarsa, ya bayyana cewa yana baiwa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf Shawarar kada yayi abinda zai kawo hargitsi a jiharsa ta Kano.
Malamin ya bayyana cewa, bai ji dadin abinda gwamnatin jihar Kano ta yi ba na sauke Aminu Ado Bayero ta nada Muhammad Sanusi II ba.
Ya jawo hankalin gwamnatin jihar ta Kano cewa, ta yiwa doka biyayya dan zaman lafiya me dorewa a jihar ta kano.
Shugaban gidauniyar ta Dahiru Bauchi, Ibrahim Dahiruin ya bayyana cewa, babu wanda yafi karfin doka.
Yayi kira ga majalisar majalisar tarayya da ta yi doka da zata hana ‘yan siyasa amfani da damarsu wajan wulakanta sarakai ta hanyar saukesu.
...
DA DUMI-DUMI: Kotu ta haramtawa Aminu Ado Bayero cigaba da bayyana kansa a matsayin Sarkin Kano, ta umurci yan sanda su fitar dashi daga fadar Nasarawa da yake ciki yanzu.
Abin jira dai a gani shine ko ‘yansandan zasu bi umarnin Kotun, ganin cewa a baya ma an samu wata kotu ta bayar da umarnin hana sauke Aminu Ado Bayero amma umarnin bai yi amfani ba?
Rigimar sarautar Kano dai ta dauki hankula sosai a kasarnan inda a karon farko aka samu sarakuna biyu a jihar da kowane ke cewa shine sarkin Kano.
Shugaban karamar Hukumar Munya ta jihar Naija, Malan Aminu Najume ya koka kan ayyukan ‘yan Bindiga a karamar hukumar tasa inda ya nemi a kubutar da mutanensa daga hannun ‘yan Bindiga.
Ya bayyana hakane ga manema labarai inda yace ‘yan Bindigar sun shiga garin kuci inda suka kashe mutane 7 da kuma sace 150.
Ya bayyana cewa, cikin wadanda aka kashe akwai jami’an tsaro 4 da kuma ‘yan Bijilante da wasu mutanen garin.
Saidai ya jinjinawa jami’an tsaron dake garin inda yace aun kashe guda 25 daga cikin ‘yan Bindigar.
Yace yawanci ‘yan Bindigar na zuwa ne daga jihar Kaduna inda suke musu aika-aika daga bisani su koma Kadunar.
Yace sun shiga garin da mashina kusan 100 kuma sun rika bi gida-gida suna daukar wanda suke son yin garkuwa dasu da suka hada da mata.
Tauraron Fina-finan Hausa kuma mawaki, Sani Musa Danja ya bayyana cewa, Tsohon sarkin Kano da majalisar jihar Kano ta sauke, Aminu Ado Bayero ya hakura ya ajiye lema da sanda ya tafi amma wasu suka zigoshi ya dawo.
Sani Musa Danja ya bayyana hakane a wani bidiyo da ya saka a shafinsa na sada zumunta inda ya yi tsokaci akan rikicin siyasar Kano.
Yace abin takaici shine duka sarakan ‘yan uwan junane amma an dauko wani abu da zai saka gaba da kiyayya a tsakaninsu.
Sani Musa Danja yayi kiran kawo abinda zai sa zaman lafiya da ci gaba ya dare a Kano.