Friday, December 19
Shadow
Kalli Hoton matar da kotu ta yankewa hukuncin kis-sa ta hanyar ra-ta-ya a jihar Kebbi saboda kash-she mijinta, saidai tace bata yadda a kash-sheta ba, zata daukaka kara

Kalli Hoton matar da kotu ta yankewa hukuncin kis-sa ta hanyar ra-ta-ya a jihar Kebbi saboda kash-she mijinta, saidai tace bata yadda a kash-sheta ba, zata daukaka kara

Auratayya, Labaran jihar Kebbi
Babbar Kotu a jihar Kebbi ta yankewa Fatima Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunta da laifin kashe mijinta Attahiru Muhammad-Ibrahim. Lamarin ya farune a ranar 25 ga watan Augusta na shekarar 2022 inda Fatima ta cakawa mijin nata wuka a ciki. Mai shari'a, Justice Umar Abubakar ne ya yanke wannan hukunci inda yace sun samu hujjoji masu karfi dake nuna cewa lallai Fatima ce ta kashe mijinta. Yace kuma an yanke mata hukuncin daurin shekaru 7 a gidan yari saboda azabtar da mijin nata da ta yi. Saidai lauyan Fatima, Sani yace zasu daukaka kara.
Likitocin jihar Yobe basu shiga yajin aikin NLC ba

Likitocin jihar Yobe basu shiga yajin aikin NLC ba

Siyasa
Likitocin jihar Yobe karkashin kungiyarsu ta (NMA) basu shiga yajin aikin kungiyar kwadago ta NLC ba a ranar Litinin. Shugaban kungiyar na jihar, Dr Abubakar Kawu Mai Mala ne ya bayyana hakan inda yace duk da yake 'yan uwa ne su da NLC amma basa karkashin kungiyar. Ya kara da cewa, kuma bangaren lafiya a jihar ta Yobe na da matukar muhimmancin da baza'a kulleshi ba gaba daya.
Gwamnatin Tarayya ta amince ta biya sama da Naira dubu 60 a matsayin mafi karancin Albashi

Gwamnatin Tarayya ta amince ta biya sama da Naira dubu 60 a matsayin mafi karancin Albashi

Siyasa
Gwamnatin Najeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da kungiyoyin kwadagon NLC da TUC a wani taron gaggawa da ta gudanar a ranar Litinin karkashin jagorancin sakataren gwamnatin kasar, George Akume a wani yunkuri na kawo karshen yajin aikin sai abinda hali ya yi da kungiyoyin kwadagon suka fara a wannan rana. Bangarorin biyu sun shafe sa’oi biyar zuwa shidda suna tattaunawa da juna kuma a karshe sun cimma matsaya a kan wasu batutuwa. Ministan yada labaran kasar Mohammed Idris ya shaida wa BBC cewa gwamnati ta amince ta yi kari a kan naira dubu 60 wanda shi ne sabon albashin mafi karanci na ma’aikata da ta gabatar wa kungiyoyin kwadagon tun farko, wanda suka yi fatali da shi. Ministan ya yi ikirarin cewa a karkashin yarjejeniyar da suka cimma kungiyoyin kwadagon sun amince su ...

Na tuba na daina maganganun Batsa, kuma Sheikh Daurawa ya sakani a Islamiya>>G-Fresh Al’amin

G-Fresh Al'amin, Nishadi
Tauraron mawaki kuma dan Tiktok, G-Fresh Al'amin ya bayyana cewa, ya tuba ya daina maganganin batsa. Ya bayyana hakane a shafinsa inda yace manya sun masa maganar rashin dacewar hakan. Saidai yace ba zai daina yaki da kamfanin dan malele ba. Ya kuma bayyana cewa Malam Aminu Ibrahim Daurawa ya sakashi a Islamiya, zai rika zuwa daukar darasi. https://www.tiktok.com/@kanostatematerial/video/7376403600743877893?_t=8mu4XA2C5oL&_r=1 A baya dai, mun ji rahoton yanda Hukumar Hizbah dake Kano ta Kama G-Fresh Al'amin bisa zarge-zarge.

KARANTA KA KARU: Falalar Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hajji

Ilimi
An karbo Hadisi daga ibn Abbas (R.A) ya ce Annabi (SAW) ya ce: ranar daya ga watan zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya gafarta wa Annabi Adam (A.S). Duk wanda ya azimci wannan rana Allah(SWT) Zai gafarta masa kowane irin zunubi tsakaninsa da Shi..(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) Ya fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi. Wanda ya azimci wannan rana yana da lada kwatankwacin wanda ya raya shekara da ibada ..(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya karbi addu’ar Annabi Zakariyya (A.S) Ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan rana Allah (SWT) Zai karbi adduo’in sa..(4) Ranar hudu ga Zulhijja ita ce ranar da aka haifi Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya azimci wannan rana Allah Zai kare shi daga talauci da m...
Da Duminsa: Kungiyar Kwadago ta NLC ta amince ta dakatar da yajin aikin da take dan ci gaba da tattaunawa da Gwamnati

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago ta NLC ta amince ta dakatar da yajin aikin da take dan ci gaba da tattaunawa da Gwamnati

Siyasa
Rahotannin da muke samu na cewa, Kungiyar Kwadago ta NLC da TUC sun amince su janye yajin aiki da suke dan ci gaba da tattaunawa da gwamnati. An samu wannan matsaya ne bayan zaman da wakilan kungiyoyin kwadagon da gwamnatin tarayya. Kungiyoyin zasu zauna da membobinsu gobe dan tattauna maganar janye yajin aikin. Gwamnatin tarayya ta amince a ci gaba da tattaunawa akan mafi karancin Albashi sama da Naira Dubu 60.
Mafarauci ya harbe abokin farautarsa inda yayi tsammanin dabbace

Mafarauci ya harbe abokin farautarsa inda yayi tsammanin dabbace

Tsaro
An kashe wani mafarauci Sunday Ijiola a Yewa jihar Ogun inda aka yi tsammanin dabbace. Atanda Agbobiado ne yayi kisan ranar 28 ga watan Mayu. Mafarauta kusan 15 ne suka fita farautar inda suka raba kawunansu a cikin daji. Da Atanda ya tabbatar da abinda ya aikata sai ya tsere. Wanda aka harba din dan kimanin shekaru 43 ya mutu akan hanyar zuwa Asibiti. Kakakin 'yansandan jihar Omolola Odutola ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace suna bincike akai.

Kungiyar kare hakkin Musulmi ta Murik ta jawo hankalin musulmai da kada su shiga yajin aiki

Duk Labarai
Kungiyar kare hakkin Musulmi ta murik ta bayyana cewa, yajin aikin da ake zai jefa rayuwar musulmai cikin wahala musamman ma ya dake fuskantar babbar Sallah. Dan haka kungiyar ta yi kira ga kungiyar kwadago data daga yajin aikin nada sai bayan sallah. Kungiyar ta bayyana hakane a sanarwar data fitar ta hannun babban daraktanta Professor Ishaq Akintola a yau Litinin. Ya bayyana cewa wannan yajin aiki zai saka musulmai wahalar ababen hawa dan haka suna kiran da a canja lokacin yin yajin aikin.