Thursday, December 18
Shadow
Hotuna da Bidiyo:Zanga-zanga ta barke a kasar Mexico inda ‘yan kasar suka fito suna goyon bayan Falasdinawa, sun yi yunkurin kona ofishin jakadancin kasar Israela

Hotuna da Bidiyo:Zanga-zanga ta barke a kasar Mexico inda ‘yan kasar suka fito suna goyon bayan Falasdinawa, sun yi yunkurin kona ofishin jakadancin kasar Israela

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Mutane akalla 200 ne suka fito a kasar Mexico inda suke nuna rashin jin dadi kan kisan da kasar Israela kewa Falas-dinawa. Mutanen sun yi arangama da jami'an tsaro inda suka rima jefawa jami'an tsaron duwatsu da wuta da suka kunna a tsumma. https://twitter.com/Megatron_ron/status/1795769204068491650?t=8ik7IoPGe4o8qQNpnKQYmA&s=19 Saidai jami'an tsaron suma sun rika jefawa masu zanga-zangar barkonon tsohuwa da kuma duwatsu.
Nawane farashin Dala a yau, 29/05/2024

Nawane farashin Dala a yau, 29/05/2024

Nawa ne farashin dala a yau
Darajar Naira ta dan fara dawowa inda a jiya, Talata aka sayi dalar Amurka akan Naira 1,173 a farashin Gwamnati. A ranar Litinin dai an sayi dalar akan Naira 1,500 ne a farashin Gwamnatin. Shi kuwa farashin Pound an saye shine akan Naira 1,888, sai kuma Euro da aka siya akan Naira 1,630. An sayi dalar Canada akan Naira 1,112. Sai kuma kudin China, Yuan an sayeshi akan Naira 150.
Kasar Saudiyya ta zuciya akan Israela inda tace Israelan na aikatawa Falas-dinawa kisan kare dangi

Kasar Saudiyya ta zuciya akan Israela inda tace Israelan na aikatawa Falas-dinawa kisan kare dangi

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Kasar Saudiyya ta yi Allah wadai da kisan da kasar Israela kewa Falas-dinawa. Ta bayyana cewa Israelan nawa Falas-dinawan kisan kare dangi. Israela ta kashe mutane akalla 21 a harin data kai kan al-Mawasi dake Rafah. Hakan ya zo ne bayan da ta kashe mutane sama da 40 a harin data kai kan wani sansanin a Rafah ranar Labadi. Ma'aikatar harkokin waje ta Kasar Saudiyya tace Israela ce ke da alhakin koma menene ke faruwa a Rafah. Kuma ta yi kiran kasashen Duniya da su dauki matakin hana wannan kisa da Israela kewa Falasdinawan.
An kashe jimullar Mutane 4,416 sannan an yi garkuwa da 4,334 a shekara 1 da Tinubu yayi yana mulkin Najeriya

An kashe jimullar Mutane 4,416 sannan an yi garkuwa da 4,334 a shekara 1 da Tinubu yayi yana mulkin Najeriya

Siyasa
Rahotanni sun bayyana cewa, an kashe jimullar mutane 4,416 da yin garkuwa da guda 4,334 a shekara 1 da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yayi yana mulki. Wata gamayyar masu fafutukar kasa da kasa da kuma Najeriya su 84 ne suka fitar da wannan rahoto. Rahoton yace kungiyoyin basu saka abubuwan dake faruwa na fashi da makami da sauran laifuka ba. Sunce wannan lamari ya sanya 'yan Najeriya sun rasa 'yancin rayuwa me inganci da kuma rayuwa cikin walwala. Kungiyar tace ci gaba da wannan lamari ya jefawa 'yan Najeriya tsoro da fargaba da rashin tabbas. Kuma sun ce idan gwamnatin Tinubu bata dauki mataki kan lamarin ba, suna daf da fitar da rahoton yanke tsammani akanta. Sunce suna jawo hankalin gwamnatin Tinubu data yi kokari wajan sauke nauyin dake kanta na kare rayuwa da dukiy...
Kamin ka samu mutum 1 da baya son mahaifina sai ka samu 10 masu sonsa>>Inji Dan Sarki Muhammad Sanusi II, Ashraf Sanusi

Kamin ka samu mutum 1 da baya son mahaifina sai ka samu 10 masu sonsa>>Inji Dan Sarki Muhammad Sanusi II, Ashraf Sanusi

Kano
Dan gidan me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, Ashraf Sanusi ya bayyana cewa kamin ka samu wanda baya son mahaifinsa guda daya, sai ka samu mutum 10 dake sonsa. Dan haka yace wanda ke son mahaifinsa sun fi wanda basa sonshi yawa. Ya rubuta hakane a shafinsa na sada zumunta. Saidai an jawo hankalinshi kan cewa, ya daina biyewa makiya, kuma ya amsa da ya gode. "You hate him if he talks, you hate him if he’s silent, you hate him if he’s happy, you hate him if he’s asleep. It’s only God that can help you and your hate. But for every one of you there’s 10 of us supporting and loving him, you’re outnumbered and sadly you’ve already lost."
Kuma Dai:EFCC ta sake kama wani matashi saboda lika Kudin Naira a wajan biki a jihar Gombe

Kuma Dai:EFCC ta sake kama wani matashi saboda lika Kudin Naira a wajan biki a jihar Gombe

Gombe
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta EFCC ta sake kama wani matashi a jihar Gombe me suna Zachariyya Muhammad saboda yin likin kudin Naira a wajan wani biki. An kama shine ranar Asabar, 24 ga watan Mayu bayan ya lika kudin Naira dari 200 a wajan wani bikin G-Connect. Ko da aka nuna masa bidiyonsa yana likin, ya amsa cewa lallai shine, hukumar zata gurfanar dashi a gaban kotu. A baya dai EFCC ta kama mutane da yawa a jihar Gombe shima.
Hoton Sojan Najeriya da aka kama ya saci harsasai

Hoton Sojan Najeriya da aka kama ya saci harsasai

Tsaro
Hukumomin soji dana CJTF a jihar Borno sun kama wani soja da laifin satar harsasai. An kama sojan ne me suna Corporal Francis Bako a tashar motar Kano dake Maiduguri. An kamashi ne bayan samun bayanan sirri akan satar harsasan da yayi. Sojan dai na kan hanyar zuwa Kadunane bayan da aka kamashi da harsasan guda 602 kuma yana tsare yanzu haka.