Wednesday, January 7
Shadow
An bayyana sunayen sojojin da Kungiyar IPOB ta kashe

An bayyana sunayen sojojin da Kungiyar IPOB ta kashe

Tsaro
Hukumar Sojojin Najeriya ta bayyana sunayen sojoji 5 da ake zargin 'yan Kungiyar IPOB sun kashe. An kashe sojojinne a ranar Laraba a Obikabia dake jihar Abia. sunayen sojojin sune: • Sergeant Charles Ugochukwu (94NA/38/1467)• Sergeant Bala Abraham (03NA/53/1028)• Corporal Gideon Egwe(10NA/65/7085)• Corporal Ikpeama Ikechukwu (13NA/70/5483)• Corporal Augustine Emmanuel (13NA/70/6663) Hukumar sojojin Najeriya dai ta sha Alwashin daukar mataki me tsauri dan rama kisan sojojin nata.
‘Ɗaliban Najeriya sama da miliyan tara ne suka nemi bashin karatu’

‘Ɗaliban Najeriya sama da miliyan tara ne suka nemi bashin karatu’

Tsaro
Asusun bayar da bashin karatu na Najeriya (NELFUND) ya ce sama da ɗalibai miliyan 9.5 ne suka kai ziyara ofishinta dangane da bashin karatu da za a bai wa dalibai tun bayan buɗe shafin da za a cike takardar neman bashin karatun a ranar Juma’ar da ta gabata. Sama da ɗalibai 6,000 ne suka cike takardan neman bashin. Yayin da yake yi wa manema labarai karin haske a taron da aka shirya wa ɗaliban da suka cike takardan neman bashin a ranar Alhamis, shugaban asusun, Akintunde Sawyerr, ya ce sama da kashi 90 cikin 100 na manyan makarantun gwamnatin tarayya sun mika bayanan dalibansu da cibiyoyi kusan biyar da suka rage. Ya kuma bayyana cewa nan da makwanni uku za a bude shafin neman bashin ga daliban da ke manyan makarantu na gwamnati domin su samu su iya cike takardun neman bashin karat...
Gwamnatin Abia ta sa ladan N25m ga wanda ya fallasa mutanen da suka kashe sojoji

Gwamnatin Abia ta sa ladan N25m ga wanda ya fallasa mutanen da suka kashe sojoji

Tsaro
Gwamnatin jihar Abia da ke kudu maso gabashin Najeriya ta saka ladan naira miliyan 25 ga duk mutumin da ya bayar da bayanan da za su taimaka a kama mutanen da suka kashe sojoji a jihar. Cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labaran jihar, Okey Kanu ya fitar, gwamnatin jihar ta aike da sakon ta'aziyya ga babban hafsan sojin kasa na Najeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja kan faruwar lamarin. A ranar Alhamis ne wasu 'yan bindiga suka afka wa sojoji a wani shingen bincike a mahadar Obikabia da ke yankin tsaunin Ogbor, tare da kona motar aikinsu. Rahotonni sun ce wasu sojojin sun samu tsallake rijiya da baya a harin. “Domin samun saukin kama maharan, gwamnati ta yi alkawarin bayar da ladan naira miliyan 25 ga duk wanda ya bayar da bayanan da za su taimaka wajen kama su,'' in ji s...
Amurka za ta tallafa don sake gina makarantu da asibitoci a Gaza – Biden

Amurka za ta tallafa don sake gina makarantu da asibitoci a Gaza – Biden

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Shugaban Amurka Joe Biden ya ce ana bukatar hanyar sasanci domin kawo karshen yakin yankin Gabas ta Tsakiya, ciki har da daidaita lamurra a kan iyakar arewacin Lebanon. Mista Biden ya ce akwai bukatar shugabannin Falasdinawa da na Isra'ila su hada kai domin sake gina Gaza, ta yadda ba za a bar Hamas ta sake mallakar makamai ba. ''Amurka za ta tallafa wajen sake gina makarantu da asibitocin Gaza'', in ji Biden. Ya kara da cewa shirin zai taimaka wajen sake daidaita lamurran dangataka da Saudiyya da magance barazanar Iran a yankin. Mista Biden ya kuma gabatar da kudurin da zai bai wa Isra'ila damar zama mai karfi a yankin.
An kulle kasuwanni da makarantu yayin da sojoji ke nema  wanda suka kashe sojoji 5 a garin Aba

An kulle kasuwanni da makarantu yayin da sojoji ke nema wanda suka kashe sojoji 5 a garin Aba

Tsaro
Garin Aba ya rikice inda sojoji suka mamayeshi bayan kisan abokan aikinsu 5. Wasu da ake kira da 'yan Bindigar da ba'a san ko su wanene ba amma ana kyautata zaton 'yan IPOB ne kawai da suke fakewa da wannan sunan suka yi kisan. Sun yi kisanne ranar Laraba bayan sun tursasa kowa ya je gida ya zauna dan tunawa da mutanen da suka mutu a yakin Biafra. Lamarin yasa hukumar sojojin Najeriya ta sha Alwashin sai ta rama wannan kisa da kakkausar murya. Rahoton jaridar Vanguard yace sojojin sun shiga kasuwanni suka tursasa mutane suka kulle shaguna da kuma a jiya, Juma'a yawanci yara basu je makaranta ba a garin. Hakanan an ga jirage masu saukar Angulu suna shawagi a sararin samaniyar wajan.
Bidiyo da Hotuna: Kalli Yanda Ali Jita da Rahama Sadau suke shakatawa a Landan

Bidiyo da Hotuna: Kalli Yanda Ali Jita da Rahama Sadau suke shakatawa a Landan

Ali Jita, Kannywood, Rahama Sadau
Taurarin Fina-finan Hausa, Rahama Sadau da Ali Jita kenan a wadannan hotunan da bidiyo suke shakatawa a kasar waje. An ga Jita da Rahama dai suna nishadi tare a cikin mota da kan titi. Ali Jita ne ya saka bidiyon a shafinsa na sada zumunta. https://www.tiktok.com/@realalijita/video/7375206383370652933?_t=8mpctjMHVyA&_r=1 Da yawan mata da maza na masana'antar Kannywood sukan je kasashen waje dan shakatawa.
Kasashen Larabawa sun sha Alwashin ba zasu bar Falas-dinawa su sake mallakar makamai ba bayan yakin su da Israela

Kasashen Larabawa sun sha Alwashin ba zasu bar Falas-dinawa su sake mallakar makamai ba bayan yakin su da Israela

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Rahotanni sun bayyana cewa, kasashen Larabawa sun dauko alwashin ba zasu sake barin Falas-dinawa au mallaki makamai ba bayan an gama yaki tsakaninsu da Israela. Hakan na zuwa ne yayin da ake tsammanin za'a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Israela da Kungiyar Hamas. Saidai abin tambaya anan shine, anya kasashen Larabawan zasu iya aikata hana Falas-dinawa mallakar makamai? Dalili kuwa shine a yanzu gashi ana ta kashesu babu kasar Larabawan data shigar musu ko ta tsaya musu, an zura ido ana kallo Israela na musu kisan kare dangi, ta yaya zasu yadda a hanasu mallakar makamai bayan sun san duk randa Israela ta sake far musu da yaki babu me tare musu? Wannan dai abune me kamar wuya.
Hotuna:Cristiano Ronaldo ya kare kakar wasan bana ba tare da kofi ba inda Al Hilal ta doke kungiyarsa ta Al Nassr, Kalli Hotuna da Bidiyonsa yana kuka, Magoya baya suna tsokanarsa ta hanyar kiran sunan Messi

Hotuna:Cristiano Ronaldo ya kare kakar wasan bana ba tare da kofi ba inda Al Hilal ta doke kungiyarsa ta Al Nassr, Kalli Hotuna da Bidiyonsa yana kuka, Magoya baya suna tsokanarsa ta hanyar kiran sunan Messi

Kwallon Kafa, Labaran Cristiano Ronaldo
Kungiyar Al Hilal ta lashe kofin King Cup na Saudi Pro League bayan doke Al Nassr da ci 5-4 a bugun daga kai sai me tsaron gida. Wannan ne kofi na biyu da kungiyar ta lashe a shekaru biyu a jere. Abin bai yiwa Cristiano Ronaldo dadi ba a wasan da aka buga jiya Juma'a a filin wasa na King Abdallah. An kammala wasan Cristiano Ronaldo yana kuka inda abokan wasansa suka rika bashi baki. https://twitter.com/centregoals/status/1796654446396797079?t=IljN_zZoTlKOgbxoo5HmzA&s=19 Da yawa dai sun ce basu taba ganin Ronaldon a cikin irin wannan halin ba. https://twitter.com/WeAreMessi/status/1796788372368699805?t=A6iDAswCtRpc0vRS7MyxFQ&s=19 A yayin da yazo fita daga Filin, magoya bayan Al Hilal sun rika kiran sunan Messi dan su bashi haushi. A karin farko a tari...
Biden ya yi kira ga Isra’ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta

Biden ya yi kira ga Isra’ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Shugaba Biden na Amurka ya yi kira ga Isra'ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita a yakin da suke yi tsakaninsu. Yarjejeniyar za ta sa jami'an Isra'ila su tsagaita wuta ta tsawon mako shida, sannan Hamas ta saki Isra'ilawan da ta yi garkuwa da su - a kuma saki Falasdinawan da ake tsare da su a gidajen yari a Isra'ila. Yarjejeniyar ta yi tanadin Isra'ila za ta janye daga yankunan Gaza sannan ta kyale a rika shiga da kayayyakin agaji. Yayin da za a a ci gaba da tattaunawa, yarjejeniyar za ta ci gaba da aiki har a kai ga sakin duka wadanda aka yi garkuwa da su. Daga nan dakarun Isra'ila su fice daga Gaza Falasdinawa su koma gidajensu su ci gaba da rayuwa.