Wednesday, February 18
Shadow
Kalli Bidiyon da Duminsa: Danbaban Gawuna ya baiwa Malam Nasiru Jaoje, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da Me martaba Sarkin Kano Hakuri

Kalli Bidiyon da Duminsa: Danbaban Gawuna ya baiwa Malam Nasiru Jaoje, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da Me martaba Sarkin Kano Hakuri

Duk Labarai
Danbaban Gawuna ya fito ya baiwa Malam Nasiru Jaoje da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da Me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II hakuri. Ya bayyana cewa duk abubuwan da suka faru a baya ya tuba ba zai kara ba kuma yana fatan za'a gafarceshi. Hakan na zuwane bayan da rahotanni a baya suka ce jami'an tsaro sun kamashi a wajan bikin murnar nadin sarautar Rarara. https://www.tiktok.com/@hon.danbabangawuna/video/7585192310754004232?_t=ZS-92KOVWGvZpo&_r=1
Kalli Bidiyon: Ni dai ban ga Aibun kalaman da Dr. Hussain yayi ba na cewa kada Allah yasa ranar Qiyama ya kai matsayin da sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ceceshi kamin ya shiga Aljannah ba>>Inji Dr. Jameel

Kalli Bidiyon: Ni dai ban ga Aibun kalaman da Dr. Hussain yayi ba na cewa kada Allah yasa ranar Qiyama ya kai matsayin da sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ceceshi kamin ya shiga Aljannah ba>>Inji Dr. Jameel

Duk Labarai
Dr. Jamilu ya goyi bayan Dr. Hussain Kano kan kalamansa na cewa yana rokon Allah kada ya kaishi matsayin da sai ya nemi taimakon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ranar qiyama kamin ya shiga Aljannah. Dr. Jamilu yace ya saurari jawabin Dr. Hussain Kano Gaba daya kuma bai gano aibu a cikin kalaman ba. https://www.tiktok.com/@isah_bello_assalafy_garo/video/7585144287533206804?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7585144287533206804&source=h5_m&timestamp=1766068645&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=andro...
Da Duminsa: Kotu taki amincewa da bayar da belin Tsohon Minista, Abubakar malami inda tace EFCC ta ci gaba da tsareshi

Da Duminsa: Kotu taki amincewa da bayar da belin Tsohon Minista, Abubakar malami inda tace EFCC ta ci gaba da tsareshi

Duk Labarai
Babbar Kotun tarayya dake Abuja ta ki amincewa da bayar da Belin tsohon Ministan shari'a, Abubakar malami inda yake neman a sakeshi daga komar EFCC. Saidai kotu a zamanta na ranar Alhamis tace EFCC ta ci gaba da tsare Malami inda Mai Shari'a, Babangida Hassan yace ci gaba da tsare Abubakar Malami bai sabawa doka ba.
Kalli Bidiyon yanda daya daga cikin sojojin Najeriya da kasar Burkina Faso ta kama ya tabbatar da cewa jirgin su tangarda ya samu shiyasa suka sauka a kasar

Kalli Bidiyon yanda daya daga cikin sojojin Najeriya da kasar Burkina Faso ta kama ya tabbatar da cewa jirgin su tangarda ya samu shiyasa suka sauka a kasar

Duk Labarai
Daya daga cikin sojoji 11 da kasar Burkina Faso ta kama tsawon kwanaki 9 bayan da jirginsu ya sauka a kasar yace, jirgin nasu da gaske tangarda ya samu. Ya bayyana hakane yayin ganawarsa da wakilan Najeriya ta tura kasar dan a baiwa shugaban kasar, Ibrahim Traore hakuri ya sakesu. Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar ne ya jagoranci tawagar. https://twitter.com/NigAffairs/status/2001594423025471848?t=_6oHc1fOg4wScDRR8smDVA&s=19