
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda ke wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya ta isa Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a yau Talata don sauraron karar da aka shigar a kanta.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Mai Shari’a Binta Nyako ta sanya ranar yau talata domin sauraron karar raina kotu da shugaban majalisar dattawa ya shigar kan Akpoti-Uduaghan.
Mai Shari’a Nyako ta dage sauraron shari’ar zuwa ranar Litinin mai zuwa domin ci gaba da sauraron karar gaba ɗaya.
- Jaridar Arewa