Tuesday, January 21
Shadow

Tinubu ya ce a kamo maharan da suka kashe mutum 50 a Katsina

Shugaba Tinubu ya umurci jami’an tsaro da su kamo maharan da suka kai hari a ƙananan hukumomin Dutsin-Ma da Kankara na jihar Katsina da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama tare da tabbatar da an hukunta su.

Shugaban ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman Ajuri Ngelale ya fitar a ranar 11 ga watan Yuni, 2024 yana mai kakkausar suka kan yawaitar hare-hare a ƙasar.

A yayin da ya bayyana sabbin hare-haren a matsayin munanan hare-hare, shugaban ya jaddada cewa za a ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaron ‘yan kasa da kuma taarwatsa ‘yan ta’adda gaba daya da sauran masu tayar da zaune tsaye da kuma baƙin ciki a kowane ɓangare na ƙasar.

Karanta Wannan  Akwai yiyuwar Shugaba Tinubu zai yiwa majalisar Zartarwarsa garambawul inda za'a yiwa wasu ministoci canji, za'a kara kirkiro da wasu

Shugaban ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, da gwamnati da kuma al’ummar jihar Katsina, tare da addu’ar Allah ya jikan waɗanda suka rasu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *