Monday, April 21
Shadow

Wanda suke bani kyauta a baya sune yanzu suke rokona in basu kudi saboda matsin tattalin arziki>>Inji Peter Obi

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi ya bayyana cewa, wadanda ke bashi kyauta a shekarun da suka gabata a yanzu sune ke neman ya tallafa musu.

Peter Obi ya bayyana hakane a wajan taron Jam’iyyar Labour party din da ya wakana a Abuja.

Yace zasu shiga zabe me zuwa a shirye kuma zasu tsayar da mutane na gari a matsayin ‘yan takara.

Peter Obi ya kara da cewa, matsin tattalin arziki yayi tsanani ta yada wanda a baya suke gayyatarsa yana cin abinci tare dasu amma yanzu sune ke neman ya taimaka musu.

Karanta Wannan  Dalilin da ya sa Gwamnatin Tarayya ba ta fara biyan kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba – ALGON

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *