Sunday, March 23
Shadow

Wane Irin Mulki Ake a kasarnan? Kasa da shekaru 2 da kama mulki har an fara yiwa Shugaba Tinubu yakin neman zaben 2027

Yayin da har yanzu gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata cika shekaru 2 da kafuwa ba, an fara yakin neman zaben 2027 dan ganin ya zarce.

Duk da yake shi shugaban kasar ko Jam’iyyar APC a hukumance basu bayyana fara yakin neman zaben ba.

Amma wasu jigo a Gwamnatin irin su shugaban Jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Sakataren Gwamnati, George Akume sun bayyana neman Shugaba Tinubu ya zarce.

A yayin da yake ganawa da wasu ‘yan Jam’iyyar a hedikwatar Jam’iyyar dake Abuja, Ganduje yace ‘yan siyasa masu son tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2027 su dakata sai bayan 2031 idan Tinubu ya gama wa’adinsa na shekaru 8 akan mulki.

Karanta Wannan  Idan Har Ɗan El-Rufai Bai Yarda Da SDP Ba, Wane Ɗan Nijeriya Ne Mai Hankali Zai Yarda Da Wannan Jam’iyya, Inji Reno Omokri

Hakanan shima Akume a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV yace yace Atiku Abubakar ya dakata da neman zama shugaban kasa a 2027.

Hakan an ga fastocin yakin neman zaben Tinubu a karo na 2 a jihohin Kebbi, Kaduna, Kwara da babban birnin tarayya, Abuja.

Tuni dai ‘yan Jam’iyyar Adawa suka fara Allah wadai da wannan mataki.

Hakan ya sabawa dokar kundin tsarin mulkin Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *