Tuesday, May 19
Shadow

Wane Irin Mulki Ake a kasarnan? Kasa da shekaru 2 da kama mulki har an fara yiwa Shugaba Tinubu yakin neman zaben 2027

Yayin da har yanzu gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata cika shekaru 2 da kafuwa ba, an fara yakin neman zaben 2027 dan ganin ya zarce.

Duk da yake shi shugaban kasar ko Jam’iyyar APC a hukumance basu bayyana fara yakin neman zaben ba.

Amma wasu jigo a Gwamnatin irin su shugaban Jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Sakataren Gwamnati, George Akume sun bayyana neman Shugaba Tinubu ya zarce.

A yayin da yake ganawa da wasu ‘yan Jam’iyyar a hedikwatar Jam’iyyar dake Abuja, Ganduje yace ‘yan siyasa masu son tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2027 su dakata sai bayan 2031 idan Tinubu ya gama wa’adinsa na shekaru 8 akan mulki.

Karanta Wannan  Wani matashi kenan daga cikin garin Bauchi, yayin da ya hau kan karfen wayar salula yace ba zai sauko ba sai Dr. Bala Wunti ya yarda zai yi takara

Hakanan shima Akume a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV yace yace Atiku Abubakar ya dakata da neman zama shugaban kasa a 2027.

Hakan an ga fastocin yakin neman zaben Tinubu a karo na 2 a jihohin Kebbi, Kaduna, Kwara da babban birnin tarayya, Abuja.

Tuni dai ‘yan Jam’iyyar Adawa suka fara Allah wadai da wannan mataki.

Hakan ya sabawa dokar kundin tsarin mulkin Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *