Friday, December 5
Shadow

YANZU-YANZU: Wani Matashi Daga Jihar Adamawa Ya Fara Tattaki Zuwa Katsina domin nuna goyon bayansa ga mawaki Dauda Kahutu Rarara, da kuma halartar gaisuwar rashin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, a garin Daura

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Fitaccen matashi Dudu Walle ya kama hanyar tafiya da ƙafa daga Adamawa zuwa Katsina domin nuna goyon bayansa ga mawaki Dauda Kahutu Rarara, da kuma halartar gaisuwar rashin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, a garin Daura.

A cewarsa, “Na yi bankwana da mutanen Adamawa, kuma idan an bani keke a hanya zan hau, amma idan babu zan ci gaba da tafiya da ƙafata.”

Al’umma da dama sun bayyana sha’awarsu da ƙarfafa masa gwiwa bisa irin wannan ƙudurinsa na nuna kauna da jajircewa.

Wane fata zaku masa?

Karanta Wannan  Karanta Abu biyar da ba ku sani ba kan Sheikh Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *