Wednesday, April 29
Shadow

Zargin wulakanta Naira: Kotu ta saka ranar da za ta yankewa Murja hukunci

Zargin wulakanta Naira: Kotu ta saka ranar da za ta yankewa Murja hukunci.

Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta dage ranar yanke hukunci kan shahararriyar ‘yar TikTok, Murja Ibrahim Kunya, har zuwa ranar 20 ga watan Mayu, bayan da masu gabatar da kara su ka nemi izini don gyara tuhumar da a ke yi mata.

Jaridar LEADERSHIP ta rawaito cewa hukumar EFCC ce ta gurfanar da Murja da tuhuma daya tak kan zargin cin zarafin Naira.

An ga Murja a wani faifen bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta tana watsar da kudi har Naira 400,000 tare da rawa a lokacin wani biki da aka gudanar a otal din Tahir Guest Palace a watan Disamba na shekarar 2024.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yanda 'yansanda suka bi sahun farar hula suka tsere yayin da bata gari suka sace akwatin zabe a wata mazaba dake jihar Ondo

Tuni dai wanda ake tuhumar ta amsa laifin da ake zarginta da shi.

A zaman kotun na ranar Talata da aka tsara domin yanke hukunci, lauyan EFCC, Musa Isa, ya nemi izinin gyara tuhumar, wanda lauyan dake kare wacce ake tuhuma, Abubakar Saka, ya ki amincewa da shi.

Saka ya ce gyaran tuhumar zai iya jinkirta shari’ar kuma ya shafi hakkin wadda ake tuhuma na samun adalci.

Ya kuma bayyana cewa tawagar lauyoyin kare Murja na bukatar isasshen lokaci domin nazarin sabon tuhumar.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Simon Amobeda, ya amince da bukatar masu gabatar da kara, sannan ya dage cigaban shari’ar har zuwa 20 ga watan Mayu.

Karanta Wannan  Kuma Dai: Kwanaki kadan bayan da EFCC ta kori jami'anta daga aiki saboda cin hanci da rashawa, Dala $400,000 da Gwalagwalai na miliyoyin Naira sun bace a ofishin EFCC din

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *