Monday, July 20
Shadow

Obaseki ya ce ba ya fargabar binciken EFCC

Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo ya ce ya samu labarin cewa EFCC za ta kama shi da zarar ya miƙa mulki a makon gobe.

Sai dai gwamnan ya ce ko kaɗan shi ba ya tsoro ko fargaba domin za a bincike shi a game wa’adin gwamnatinsa, kamar yadda jaridar Thisday ta ruwaito shi yana faɗa a taron EdoBEST da aka yi a Abuja.

“Na samu labarin cewa EFCC za ta kama ni makon gobe. Duk inda suka ajiye ni, zan yi amfani da damar domin gudanar da bincike.

“Mun yi aikace-aikace muhimmai, sannan mun ba mutanen jihar Edo da abubuwan da suka fi buƙata muhimmanci. Don haka me zai sa in yi fargaba? na yi abin da zan iya yi, amma za su iya zuwa su ci gaba da bi-ta-da-ƙullin da za su yi, wannan matsalarsu ce.”

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: A gidana kowa abinci kala daya yake ci, Tun daga Megadi, Direba har ni duk kalar abincin dana ci shi zasu ci>>Inji Shahararren Mawakin, Davido

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *