
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, har yanzu bai amsa tambaya ko daya ba cikin Tambayoyin da ICPC suke masa.
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai dai ya shafe kusan sama da sati biyu kenan a hannun ICPC tun da suka karbeshi daga hannun EFCC.
Ya bayyana cewa, dalilin da yasa ya ki amsa tambayoyin nasu shine binciken da ake masa na da alaka sa diyasa.
A baya dai ICPC ta kai samame gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda tace ta gano abubuwa da yawa ciki hadda wata na’ura ta yiwa waya kutse.
A baya dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi ikirarin yiwa wayar me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse.