
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikawa majalisar Dattijai da bukatar ciwo bashin dala Miliyan $516.
Shugaban ya aika da bukatar ne a yau, Alhamis inda yace za’a yi aikin gina titin Sokoto-Badagry ne da kudaden.
Kakakin majalisar, Godswill Akpabio ya bayyana cewa akwai bukatar a gaggauta amincewa da karbo bashin.
Ya bayyana cewa, ya baiwa kwamitin kula da bashi na majalisar umarnin su kammala amincewa da bashin cikin sati daya.