
Mawallafin jaridar Sahara reporters, Kuma dan Fafutuka, Omoyele Sowore ya hadu da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami inda yake tambayarsa shima ya ji yanda ake ji koh idan ana zaluntar mutum.
Sowore yace Malami haka ya rikawa mutane a lokacin yana ministan shari’a yanzu shima abin ya zo kansa.
Saidai ya jinjinawa Malami da cewa bai razana ba da abinda ake masa.
Shima Malamin ya mayar masa da raddin cewa, lallai bai tsorata ba dan duk zaman kotun da za’a yi sai ya halarta.