
A yayin da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya fito ya bayyana tabbacin hadewarsa da Peter Obi inda yace zai masa mataimakin shugaban kasa a takarar 2027.
Rahotanni daga Marali Radio TV sun bayyana cewa, Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya tonawa Kwankwaso Asiri kan yanda yakewa Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu aiki a boye.
A cewar kafar, Malam Ibrahim Shekarau yace gara su a bayyane sukewa Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu aiki, amma shi Kwankwaso ai a boye yakewa shugaban aiki.
Zuwa yanzu dai Kwankwaso bai ce uffan kan wannan zargi ba.
