
Tauraron mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ya bayyana cewa, Kiran da Atiku Abubakar ya yi a lokacin da aka sace mahaifiyarsa cewa a saketa cutar dashi yayi.
Yace suna daf da karbota sai Atiku ya wallafa a kafar sada zumunta cewa a saki mahaifiyarsa.
Yace Atiku na fadin hakan sai wasu mutanen dajin suka je suka fanshi mahaifiyar tasa a hannun wadanda ke rike da ita.
Yace hakan yasa aka kara daukar lokaci me tsawo kamin kubutar da mahaifiyar tasa.