
Dan Siyasa Aminu Warkal ya fito yawa matarsa martani bayan da ta zargeshi da rashin kaita Asibiti da rashin bata abinci.
Warkal yace tabbas tsohuwar matarsa ce kuma sun rabu sannan a cikin abubuwan data fada akwai gaskiya akwai kuma karya.
Yace maganar abinci yace ko makwabta ko almajirai dake shiga gidansa sun san akwai abinci a gidansa.
Yace dan haka zargi ne maras tushe da tace baya bata abinci.
Yace maganar kin kaita Asibiti kuma yace mahaifiyarta da ‘yan uwanta sun je gidansa suka zauna tsawon watanni 3 Kuma mahaifiyarta bata da lafiya hakanan kanwarta ma duka shi ya rika kashe kudi aka kula dasu.