
Ordinary President, Ahmad Isa yayi zargin cewa an canjawa DPO din maraban jos wajan aiki inda aka mayar dashi unguwar Kurmin Mashi.
Yace mutanen Unguwar Kurmin Mashi ne suka kirashi suka sanar dashi hakan inda suka ce ba zasu yadda ba, zasu fito zanga-zanga.
DPO din dai shine ake zargin ya mika Ummulkhairi Malamar Islamiyya wajan mafusata suka mata aika-aika.
Inda yace ba zasu yadda ba ace ba a binciki DPO din ba kuma ba’a hukuntashi ba ace an canja masa wurin aiki.