Sunday, December 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyo: Sai yanzu na yadda da masu cewa Sheikh Nura Khalid yana zuwar Wiywiy, inaga kamin yace Sufayene suke fi son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya dan kurbi Shayin Wiywiy din da ya saba sha>>Inji Malam

Kalli Bidiyo: Sai yanzu na yadda da masu cewa Sheikh Nura Khalid yana zuwar Wiywiy, inaga kamin yace Sufayene suke fi son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya dan kurbi Shayin Wiywiy din da ya saba sha>>Inji Malam

Duk Labarai
Maganar Malam Nura Khalid ta cewa Sufaye ne suka fi son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ta jawo cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta. Daya daga cikin malaman Izala ya mayar masa da raddi inda yace sai yanzu ya yadda cewa Malam Nura Khalid na zuhkar Wiywiy kamar yanda aka fada a baya. Yace kuma yana ga kamin yayi waccan magana ya sha shayin wiwi din da ya saba sha. Yace Malam Nura Khalid Jahili ne sannan abinda yasa ba zai yi wata kakkausar magana akansa ba dan kada dansa ya fito yayi kuka, kamar yanda a baya da aka ce yana shan Wiywiy ya fito ya rika kuka a social media. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7558571476857785611?_t=ZS-90PUuFzQQhU&_r=1
Bama son A gina mana makarantu ko Tituna, A samar mana da tsaro kawai>>Inji Sanata Garba Musa Maidoki daga jihar Kebbi

Bama son A gina mana makarantu ko Tituna, A samar mana da tsaro kawai>>Inji Sanata Garba Musa Maidoki daga jihar Kebbi

Duk Labarai
Sanata Garba Musa Maidoki daga jihar Kebbi ya bayyana cewa, basa bukatar a samar musu da makarantu ko tituna a jiharsu. Sanatan yace matsalar tsaro ta yi kamari a yankinsu ta yanda ya zu abinda kawai suke bukata shine tsaron ba wai a gina musu titi ko Makarantu ba. Ya bayyana hakane yayin zaman majalisar. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1975918730048876615?t=qIRYNyO0HFO_a_SoI9HFxg&s=19
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya saka hannu dan samar da makarantar horas da ‘yansanda ta musamman da zata dace da zamani

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya saka hannu dan samar da makarantar horas da ‘yansanda ta musamman da zata dace da zamani

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa dokar bude makarantar horas da 'Yansanda ta musamman hannu. Makarantar me sunan Nigeria Police Training Institutes zata horas da 'yansanda ne game da yanda zasu rika gudanar da ayyukansu daidai da zamani. Masana sun ce wannan sabuwar makarantar ka iya zama ta farko wajan kawo gyara ga ayyukan tsaro a kasarnan
Nima ina goyon bayan a saki Nnamdi Kanu>>Inji Atiku Abubakar

Nima ina goyon bayan a saki Nnamdi Kanu>>Inji Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben shekarar 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, yana kira a saki shugaban Kungiyar 'yan Ta'addha ta ÌPÒB dake son kafa kasar Biafra, watau Nnamdi Kanu. Atiku yace ci gaba da rike Nnamdi Kanu kamar budadden ciwo ne ga 'yan Najeriya dake ci gaba da yiwa mutane zafi. Sannan kuma sabawa doka ne. Yace kin bin umarnin kotu data bayar da belinsa kama karyane da kuma take hakki. Atiku yace dan haka yana goyon bayan Zanga-zangar da Sowore ya shirya ta neman a saki Nnamdi Kanu. Yace Najeriya ta gaza idan aka ci gaba da kyale Nnamdi Kanu a tsare
Mun samu ci gaba sosai, Yanzu an daina kiran Najeriya da kasar Cin Hanci da rashawa>>Inji Matar Shugaban kasa, Oluremi Tinubu

Mun samu ci gaba sosai, Yanzu an daina kiran Najeriya da kasar Cin Hanci da rashawa>>Inji Matar Shugaban kasa, Oluremi Tinubu

Duk Labarai
Matar shugaban kasa, Oluremi Tinubu ta bayyana cewa, an samu ci gaba sosai a mulkin Mijinta, Bola Ahmad Tinubu. Ta bayyana cewa, a yanzu an daina kiran Najeriya da kasar cin hanci da rashawa. Tace idan ta fita zuwa kasashen waje, aka ce daga Najeriya take mutane na son magana da ita. Ta bayyana hakane a yayin ziyarar da ta kai jihar Gombe inda ta kaddamar da wasu ayyukan ci gaba. Ta yi kira ga 'yan Najeriya dasu mayar da hankali wajan yada labarai masu kyau game da kasar.
Yayin da Gwamnatin Tarayya tace Karyace, Kungiyar kiristocin Najeriya, CAN tace maganar da Amurka ta yi na cewa ana shekye kiristoci da yawa a Najeriya gaskiyane

Yayin da Gwamnatin Tarayya tace Karyace, Kungiyar kiristocin Najeriya, CAN tace maganar da Amurka ta yi na cewa ana shekye kiristoci da yawa a Najeriya gaskiyane

Duk Labarai
Kungiyar kiristocin Najeriya, CAN ta goyi bayan kasar Amurka da ta ce ana kashe kiristoci a Najeriya da yawa. Shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh ne ya bayyana hakan ranar Laraba. Yace kin fadawa kai gaskiya da zargi ba zai kawo karshen matsalar ba Yace karfin hali da fuskantar matsalar tare ne zai kawo yadda da juna a tsakani. Yace tabbas Kiristoci a sassa daban-daban na Najeriya musamman yankunan Arewa na fuskantar Kisa da asarar Dukiyoyi da sauransu. Sanatan kasar Amurka, Ted Cruz ne ya bayyana hakan inda yayi zargin cewa an kashe Kiristoci 52,000 da kona coci-coci 20,000 a Najeriya. Gwamnatin Tarayya dai Tuni ta karyata wannan ikirarin na satan kasar Amurkar.
Kwana daya bayan da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya jinjinawa Gwamnatin Tinubu bisa farfado da tattalin arzikin Najeriya, Bankin Duniya yace duk da kokarin Gwamnati na farfado da tattalin arzikin, Mutane Miliyan 139 ne suka tsunduma cikin bakin Talauci a Najeriya

Kwana daya bayan da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya jinjinawa Gwamnatin Tinubu bisa farfado da tattalin arzikin Najeriya, Bankin Duniya yace duk da kokarin Gwamnati na farfado da tattalin arzikin, Mutane Miliyan 139 ne suka tsunduma cikin bakin Talauci a Najeriya

Duk Labarai
Bankin Duniya wanda shine gaba-gaba wajan baiwa Najeriya bashi yace mutane Miliyan 139 sun tsunduma cikin bakin Talauci a Najeriya. Bankin yace hakan na zuwane duk da ikirarin da Gwamnatin tarayya ke yi na cewa an samu habakar tattalin arziki. Bankin yace Gwamnatin sai ta kara himma wajan tabbatar da cewa Talaka na shaida wannan habakar tattalin arzikin da ake cewa an samu idan ana son a ga canji. Daraktan Bankin Duniya a Najeriya, Mathew Varghis ne ya bayyana hakan ranar Laraba a Abuja wajan taron bayyana ci gaban da aka samu. Ya jinjinawa Gwamnatin tarayya bisa ga cire tallafin man fetur da daidaita chanjin Naira zuwa kudaden kasashen waje wanda yace hakan matakai ne da zasu zama ginshikai wajan ci gaban Najeriya. Wannan bayani na bankin Duniya na zuwane kwana daya baya...
Kalli Bidiyo: Abubuwa na ci gaba da kankama a shirin sabuwar wakar Soja Boy wadda yake yi da Tsohuwar me saka Hijabi, Iftihal Madaki

Kalli Bidiyo: Abubuwa na ci gaba da kankama a shirin sabuwar wakar Soja Boy wadda yake yi da Tsohuwar me saka Hijabi, Iftihal Madaki

Duk Labarai
Tauraron me wakokin batsa na Arewacin Najeriya, Soja Boy na ci gaba da daukar Bidiyon sabuwar wakar sa wadda yake yi da Iftihal Madaki wadda aka saba gani da Hijabi a baya. Bidiyon da Soja Boy da Iftihal Madaki ke sakawa a shafukansu na sada zumunta na ci gaba da daukar hankula sosai. https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7558963301598727432?_t=ZS-90OmmeoEiFF&_r=1 Kalli Bidiyon anan A baya dai Iftihal Madaki ta dauki hankula bayan da aka ganta a wata waka tana rawa da ba'a saba ganin tana yin irinta ba. Saidai a karo na biyu gashi an sake ganinta a Bidiyon wakar Soja Boy.
Ji yanda aka kama wani Barawon waya da ya sace wayar wata mata tana bacci amma bai kashe wayar ba, data kira yace sai ta bashi dubu 50

Ji yanda aka kama wani Barawon waya da ya sace wayar wata mata tana bacci amma bai kashe wayar ba, data kira yace sai ta bashi dubu 50

Duk Labarai
Wani barawo ya sace wayar wata mata yayin da take tsaka da bacci. Saidai be kashe wayar ba. Da me wayar ta kira, sai yace zai bata amma sai ta bashi dubu hamsin. Saidai tace masa bata da Dubu 50. Amma tace idan yana so zata bashi kanta. Aikuwa sai ya yadda. Tuni dai an kamashi, lamarin ya farune a Ikotun, dake jihar Lagos. https://twitter.com/stilldey4u/status/1975825042433790433?t=BKJonJHQDeI_6w3vR9tCJg&s=19
Kalli Bidiyo: Ana ci gaba da daukar sabuwar wakar Soja Boy inda aka ga Bidiyo yana kama Khugun Iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta da Hijabi

Kalli Bidiyo: Ana ci gaba da daukar sabuwar wakar Soja Boy inda aka ga Bidiyo yana kama Khugun Iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta da Hijabi

Duk Labarai
Ana ci gaba da daukar Bidiyon sabuwar wakar Soja Boy wadda suka yi Bidiyon ta tare da iftihal Madaki wadda a baya aka saba ganinta sanye da Hijabi a Bidiyon ta. A Bidiyon an ga yanda Soja Boy ya kamo Kugun Iftihal yayin da take sanye da doguwar bakar Riga. A wakar da suka yi da ita ta farko, Iftihal ta jawo cece-kuce sosai bayan ganinta tana rawa ba Hijabi. https://www.tiktok.com/@bigdoxxx/video/7558599404547083536?_t=ZS-90NSeHnCzIX&_r=1