Thursday, March 5
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Ganin dan fafutukar neman kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa yanawa APC yakin neman zabe ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Ganin dan fafutukar neman kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa yanawa APC yakin neman zabe ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga Sunday Igboho, dan fafutukar kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa da yayi kaurin suna a shekarun baya yanawa jam'iyyar APC yakin neman zabe. A lokacin Mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Sunday Igboho tserewa yayi daga Najeriya saboda ana shirin kamashi da ake Amma yanzu ya dawo ya shiga cikin 'yan siyasa na APC. https://twitter.com/i/status/2028925681162174958 Musamman Inyamurai na ta suka suna cewa me zai sa a bar Sunday Igboho na yawo yayin da aka tsare Nnamdi Kanu.
Masu zagin Janar TY Danjuma cewa bai son Musulmi dana fito takarar gwamna a jihar Zamfara ya bani kyautar dala $500,000 saboda idan na ci zabe in magance matsalar tsaro>>Sanata Dansadau

Masu zagin Janar TY Danjuma cewa bai son Musulmi dana fito takarar gwamna a jihar Zamfara ya bani kyautar dala $500,000 saboda idan na ci zabe in magance matsalar tsaro>>Sanata Dansadau

Duk Labarai
Sanata Saidu Muhammad Dansadau ya bayyana cewa, ba gaskiya bane zagin da akewa Janar TY Danjuma cewa bai son Musulmi. Ya bayyana hakane a wajan wa'azin da yake a masallacin Apo Legislative Quarters. Yace da yake sun yi Sanata tare da matar TY. Danjuma, ta rika bashi labarin cewa da zai samu gwamnan Zamfara da an magance matsalar tsaro. Yace da ya fito takara sai matar TY Danjuma ta gaya masa cewa ga wanda yake bashi labari. Yace Janar TY Danjuma ya aika masa Tallafin dala $500,000. https://www.tiktok.com/@nassmosque1/video/7612717779065523477?_r=1&_t=ZS-94PD7DWkrT7
Hukumar DSS ta kama jami’anta saboda zargin karbar cin hanci a hannun Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Hukumar DSS ta kama jami’anta saboda zargin karbar cin hanci a hannun Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar DSS ta kama jami'anta bisa zargin sun karbi cin hanci a hannun malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Hukumar tace jami'an nata sun karbi cin hancinne inda suka kyale Malam Nasiru suka ki kamashi a filin jirgi yayin da ya dawo Najeriya a kwanakin baya. A wancan lokacin dai an ga yanda mutane suka taru suka hana kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Matar nan da ta zargi Ministan ayyuka, David Umahi da neman su yi soyayya duk da tana da aure kuma yaki biyanta kudin aikin da ta masa, ta wallafa hotunan manyan mutanen da ta yi aiki tare dasu

Matar nan da ta zargi Ministan ayyuka, David Umahi da neman su yi soyayya duk da tana da aure kuma yaki biyanta kudin aikin da ta masa, ta wallafa hotunan manyan mutanen da ta yi aiki tare dasu

Duk Labarai
Matarnan data zargi Ministan ayyuka, David Umahi da kin biyanta kudin aiki da ta masa, sannan ya nemi su yi soyayya duk da yasan tana da aure, ta wallafa hotunan manyan mutanen da tawa aiki a baya. Ciki kuwa hadda tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da Me martaba sarkin Kano, Muhammad Sanusi II. Da sauran manyan mutane da aka gani a hotunan data wallafa. https://twitter.com/i/status/2028765500876976567 Matar dai tace shekaru 12 kenan tun da tawa David Umahi aiki amma yaki biyanta hakkinta.
Matar Tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta bayyana kayan aikinta da ICPC suka dauka da suka je bincike gidan mijinta wanda a tunaninsu shine na’urar yiwa waya kutse

Matar Tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta bayyana kayan aikinta da ICPC suka dauka da suka je bincike gidan mijinta wanda a tunaninsu shine na’urar yiwa waya kutse

Duk Labarai
Matar tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta wallafa a shafinta cewa, ICPC sun dauke mata na'urar da take amfani da ita a banki. Tace tana rantsuwa da Allah na'urar ba ta kutsen waya bace. Ta bayyana cewa, cikin kayan da ICPC suka bayyana cewa sun dauka daga gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, sun manta su bayyana wannan na'urar tata. https://twitter.com/i/status/2028773296997556584 ICPC dai sun bayyana wayoyi da kwamfutocin tafi da gidanka a matsayin abubuwan da suka gano a gidan malam Nasiru Ahmad El-Rufai. A baya kuma sun zargi cewa, sun gani na'urar yiwa waya kutse.
Kalli Bidiyon: Yanda wani dan kasar Ghana ya hadu da shugaban kasar UAE suka gaisa yayin da shugaban ke ran gadi

Kalli Bidiyon: Yanda wani dan kasar Ghana ya hadu da shugaban kasar UAE suka gaisa yayin da shugaban ke ran gadi

Duk Labarai
Wani dan kasar Ghana da ya je kasar UAE ya hadu da shugaban masar UAE Sheikh Mohamed bin Zayed ya mika masa hannu suka gaisa. Shugaban ya tambayeshi daga wace kasa yake? Yace masa daga Ghana, yace masa yana cikin farin ciki? Yace masa Eh. https://twitter.com/i/status/2028536635357536257 Lamarin yasa ana ta yabawa shugaban na UAE saboda rashin girman kansa.
Da Duminsa: ICPC sun bayyana abubuwan da sua gano a gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Da Duminsa: ICPC sun bayyana abubuwan da sua gano a gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar ICPC ta bayyana kayayyakin data gano a gidan tsohon gwamnan jihar Kadunaz Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. A baya dai ICPC tace ta gano na'urar yiwa waya kutse a gidan na Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. A sanarwar da ICPC ta fitar tace ta gano Wayoyi da kwamfutoci da sauransu da suka hada da Blackberry, Nokia N95, Toshiba, Samsung IDEOS, Google IDEOS, da kuma karin wasu na'urorin hannu guda 18. Sanarwar tace an nade wadannan abubuwan ana bicike akansu. Saidai wani abu da ya dauki hankulan mutane shine cikin abubuwan da ICPC tace ta gano babu wata na'urar yiwa waya kutse a cikinsu.
Dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bello El-Rufai ya fallasa abinda ICPC kewa mahaifinsa na rashin kyautawa yayin da suke tsare dashi

Dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bello El-Rufai ya fallasa abinda ICPC kewa mahaifinsa na rashin kyautawa yayin da suke tsare dashi

Duk Labarai
Dan gidan tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Bello El-Rufai ya bayyana cewa tunda jami'an tsaro suka kama mahaifinsa, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yaki musu magana. Yace abinda kawai mahaifinsu ke gayawa jami'an tsaron shine idan suna da wani abu da suke zarginsa dashi, su kaishi kotu. Yace shirun da mahaifin nasa yayi yasa jami'an tsaron na bayyana hakan da rashin basu hadin kai, yace amma kundin tsarin mulki kasa ne ya baiwa mahaifin nasa wannan dama. Yace dalili kenan ma da yasa ICPC din suke shirya karya suna jinginawa mahaifin nasa. Hakan na zuwane bayan da ICPC suka ce sun gano na'urar yiwa waya kutse a cikin gidan Nasiru El-Rufai. Saidai Tuni iyalan Malam Nasiru suka fitar da sanarwa inda suka karyata hakan. Itama Matar Malam Nasiru, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai tace a ...