Wednesday, December 24
Shadow

Author: Bashir Ahmed

An kama malamin jami’a saboda wallafa Bidiyon rawa na dan Gwamnan Bauchi

An kama malamin jami’a saboda wallafa Bidiyon rawa na dan Gwamnan Bauchi

Duk Labarai
Kotu a jihar Bauchi na shirin yanke hukunci kan wani malamin jami'a da ya wallafa tsohon Bidiyon dan gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad yana rawa. A yau Alhamis ne ake sa ran kotun zata yanke hukuncin neman belin malamin me suna Dr. Abubakar Ahmad wanda dan gwamnan me suna Shamsudeen Bala Mohammed ne ake zargin ya shigar dashi kara. Malamin na koyarwa ne a kwalejin Federal College of Horticulture dake jihar. An kamashi ne saboda wani tsohon Bidiyon da ya wallafa na dan Gwamnan da matarsa suna rawa. Me ikirarin kare hakkin bil'adama kuma mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore ne ya wallafa hakan. Yace An tsare malamin makarantar na tsawon makonni 2 bisa cin zarafi da rashin adalci. Matar malamin me suna Fatima ta nemi a saki mijinta. Fatima ta yi kira ga Gw...
Duk Abinda shugaba Tinubu ya sani zan aikata dari bisa dari saboda ina masa biyayya sosai>>Sanata Barau Jibrin

Duk Abinda shugaba Tinubu ya sani zan aikata dari bisa dari saboda ina masa biyayya sosai>>Sanata Barau Jibrin

Duk Labarai
Sanata Barau Jibrin ya bayyana cewa yana matukar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu biyayya. Yace duk abinda yasa shi ya aikata zai aikata dari bisa dari. Yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gyara barakar siyasa ta cikin gida data kunno kai a jihar Kano kuma ya taimaka masa wajan zama mataimakin kakakin majalisar Dattijai. Ya bayyana hakane game da wata kungiya data ce tana son shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya daukeshi a matsayin mataimakinsa a zaben shekarar 2027. Jibrin yace bai san wannan kungiyar ba amma yana godiya da nagartarsa da suka duba. Yace kuma a bar maganar yanzu saboda yanzu lokacin mulki ne ba lokacin siyasa ba.
Bidiyo: Ba haka ake aiki ba, wannan zubar da mutunci ne>>Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi Allah wadai da yanda wasu ‘yansanda suka yiwa wata jarumar fina-finan kudu da ta yi shigar banza rakiya

Bidiyo: Ba haka ake aiki ba, wannan zubar da mutunci ne>>Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi Allah wadai da yanda wasu ‘yansanda suka yiwa wata jarumar fina-finan kudu da ta yi shigar banza rakiya

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta nuna rashin jin dadinta game da abinda wasu jami'anta suka aikata na yiwa jarumar fina-finan kudu, Angela Okorie rakiya yayin da take sanye da shigar banza take gudu. Bidiyon nata ya watsu sosai a kafafen sada sumunta wanda hakan ya jawo cece-kuce. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1933204045562581459?t=O4C3uPPz_0kZM96RndY-lg&s=19 Dan haka hukumar 'yansandan ta fitar da sanarwar cewa abinda 'yansandan suka aikata baya cikin tsarin aikin dansanda. Hukumar tace tana kan Bincike kuma zata dauki matakin da ya dace bayan kammala binciken lamarin.
Kalli Bidiyo: A baibul an gaya mana cewa dolene Miji ya tabbatar yana biyawa matarsa bukatar Jìmà’ì, idan ba haka ba, zata iya cin amanarsa>>Inji Wannan Matar

Kalli Bidiyo: A baibul an gaya mana cewa dolene Miji ya tabbatar yana biyawa matarsa bukatar Jìmà’ì, idan ba haka ba, zata iya cin amanarsa>>Inji Wannan Matar

Duk Labarai
Wannan matar ta bayyana cewa, a baibul an gayawa mazaje au biyawa matansu bukatar Jima'i dan kaucewa cin amana. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1937827279239098637?t=A0DINMbjdxhjB2h3J5Dthg&s=19 Ta bayyana cewa, kuma jikin mace an ce musu ba nata bane, na mijinta ne hakanan shima namijin ba nasa bane na matarsa ne.
Ni ne gatan ‘yan Najeriya, Duk wani da zai zo ya ce muku zau kayar dani zabe a 2027 kada ku saurareshi>>Shugaba Tinubu

Ni ne gatan ‘yan Najeriya, Duk wani da zai zo ya ce muku zau kayar dani zabe a 2027 kada ku saurareshi>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ce gatan 'yan Najeriya inda yace kada su saurari masu cewa zasu kayar dashi zabe a 2027. Shugaban yace 'yan adawar dake hada kai da zummar kayar dashi zabe 'yan gudun hijirar siyasa ne. Shugaban ya bayyana hakane ranar Laraba a yayin ziyarar da ya kai jihar Nasarawa ta kwana daya. Ya yabawa gwamnan jihar, Abdullahi Sule kan aikin da yakewa mutanen jiharsa inda yace zai tallafa masa da dukkan wani aikin ci gaba da zai kawo.
A yau shugaba Tinubu zai sakawa sabbin dokokin Haraji hannu

A yau shugaba Tinubu zai sakawa sabbin dokokin Haraji hannu

Duk Labarai
A yau, Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sakawa sabbin kudirin dokokin Haraji hannu a fadarsa dake Abuja. Hakan na kunshene cikin sanarwar da kakakin shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar. Kudirin dokokin guda 4 ne wanda tuni majalisar tarayya ta amince dasu bayan cece-kuce da suka jawo sosai. Shuwagabannin majalisar tarayya da shuwagabannin kungiyoyin gwamnoni da ministan kudi da sauran manyan ma'aikatan Gwamnati ne zasu shaida wannan lamari a fadar shugaban kasar kamar yanda sanarwar ta tabbatar.
TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir

TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir

Duk Labarai
TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir. Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Nijeriya Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya ce ba zai goyi bayan Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 ba, idan har Tinubu ya sauya mataimakinsa, Kashim Shettima. Jingir ya bayyana cewa matsayar shi ita ce goyon baya ga Tinubu–Shettima ne kawai. Idan Tinubu ya yanke shawarar sauya Shettima da wani daga cikin mataimakinsa.