Wata Sabuwa, Rahotanni daga (ICIR) sun ce Shugaba Tinubu bashi da Lafiya rabon da a ganshi a office tun 1 ga watan Augusta
Kafar ICIR tace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bashi lafiya kuma ana shirin fita dashi kasar waje neman magani.
Saidai me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya musanta hakan inda yace shugaban na nan qalau.
Rabon da a ga shugaba Tinubu a bainar jama'a dai tun ranar 1 ga watan Augusta wanda hakan ne yasa ake rade-radin cewa bashi da lafiya.
Hakanan an dage zaman majalisar zartaswa wadda shugaban kasar ke jagorabta a fadarsa.
Kafar ta (ICIR) tace saboda rashin lafiyar ta shugaba Tinubu, ya nada mataimakinsa, Kashim Shettima ya jagoranci gudanar da ayyuka a madadinsa.
Saidai me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga yace shugaba Tinubu ya zabi ya rika aiki daga gidane, kuma babu wata matsala game da hakan.
Game da daga zaman majalisar zartaswa kuwa, Bayo Ona...








