Saturday, April 4
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kungiyar dattawan Arewa sun nemi shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan matsalar tsaron Arewa

Kungiyar dattawan Arewa sun nemi shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan matsalar tsaron Arewa

Duk Labarai
Kungiyar dattawan Arewa ta NEF sun nemi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ayyana dokar ta baci akan matsalar tsaron Arewa. Kungiyar dattawan sun kuma yi Allah wadai da kisan sojoji 20 a kananan hukumomin Bangi, Mariga dake Jihar Naija. A sanarwar da kakakin kungiyar, Prof Abubakar Jiddere ya fitar, yace kisan sojojin alamace ta rashin tsaro a Arewacin Najeriya. Yace irin wannan hari alamace ta kaddamar da yaki akan Najeriya da 'yan ta'addar suka yi.
Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Duk Labarai
Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya ta YIAGA Africa ta ce babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027 na fuskantar barazana saboda ƙaruwar talauci da rashin tsaro a ƙasar. YIAGA ta bayyana haka ne a Abuja a lokacin da take gabatar da rahoton bincikenta, inda daraktan ƙungiyar, Samson Itodo ya ce talaucin da ya wa ƴanƙasar katutu zai iya jawo ƙaruwar sayen ƙuri'a a zaɓen, musamman ta hanyar amfani da abinci domin sayen ƙuri'a. Ya ce, "wannan zaɓen akwai alamar a yi amfani da kuɗi sama da zaɓukan baya. Yanayin talauci da yunwar da ƴanƙasar ke ciki zai sa a samu sauƙin sauya tunanin masu zaɓe," in ji shi, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito. Rahoton ya ƙara da cewa maimakon matsin tattalin arzikin da ƙasar ke ciki ya sa mutane su fusata su ...
Tsohuwar Ajiya, Ji Amsar da marigayi Aminu Dantata ya bayar da aka nemi ya tsaya takarar shugaban kasa

Tsohuwar Ajiya, Ji Amsar da marigayi Aminu Dantata ya bayar da aka nemi ya tsaya takarar shugaban kasa

Duk Labarai
Duk da cewa Aminu Ɗantata ya fi shahara a fannin kasuwanci da kuma tallafa wa jama'a, ya kuma taɓa harkokin siyasa tun daga shekarun 1963. Ya taɓa zama ɗanmajalisar wakilai a tsohuwar jihar Kaduna na wa'adi ɗaya lokacin Jamhuriya ta Farko daga 1963 zuwa 1966. Bayan kifar da gwamnatin farar hula ta lokacin ne kuma ya koma Kano, inda gwamnan mulkin soja Audu Bako ya naɗa shi kwamashinan harkokin kasuwanci a 1968. Ɗantata ya ce yayin da ake shirin shiga Jamhuriya ta Biyu, sai wasu mutane da dama suka fara neman ya tsaya takarar shugaban ƙasa. Wasu kuma sun nemi ya tsaya takarar gwamnan Kano, cikinsu har da tsohon ɗan gwagwarmaya kuma ɗansiyasa Mallam Aminu Kano. Sai dai bai amince da kiran nasu ba. "Dalilin da ya sa na ƙi yarda shi ne, a matsayina na ɗankasuwa ina ganin Allah y...
Ni Na Yì Aikì Aka Kori Ganduje Daga Shugabancin APC, Da Taĺò-Ťàĺo Ma Na So Na Mayàŕ Da Shì Aka Ba Ni Hakuri, Inji Wani Malami Dan Jihar Borno

Ni Na Yì Aikì Aka Kori Ganduje Daga Shugabancin APC, Da Taĺò-Ťàĺo Ma Na So Na Mayàŕ Da Shì Aka Ba Ni Hakuri, Inji Wani Malami Dan Jihar Borno

Duk Labarai
Ni Na Yì Aikì Aka Kori Ganduje Daga Shugabancin APC, Da Taĺò-Ťàĺo Ma Na So Na Mayàŕ Da Shì Aka Ba Ni Hakuri, Inji Wani Malami Dan Jihar Borno. Wannan Malami dan asalin jihar Borno ya ce ya so mayar da tsohon Gwamnan jihar Kano kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje tàlò-tàĺì amma aka ba shi hakuri. Malamin ya ce duk wanda ya ce zai taba Kashim Shattima to lallai za su saka kafar wando daya da shi. Hakazalika, malamin ya gargadi mataimakin shugaban majalisar dattawa na kasa, Sanata Barau Jibril da ya shiga taitayinsa, idan kuma ba haka ba zai mayar da shi Ràķùmin daji. Daga S-bin Abdallah Sokoto
Ya kamata ka mayar da hankali wajan yaki da talauci>>Gwamnonin APC suka gayawa shugaba Tinubu

Ya kamata ka mayar da hankali wajan yaki da talauci>>Gwamnonin APC suka gayawa shugaba Tinubu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnonin jam'iyyar APC sun baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar mayar da hankali wajan yaki da Talauci. Sun bayyana hakane a wata sanarwa da suka fitar ta bayan taron da suka yi a garin Benin City na jihar Edo. Shugaban kungiyar gwamnonin ta APC, gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ne ya bayyana hakan a jawabin da ya karanto. Gwamnonin sun goyi bayan tayar da komadar tattalin arziki da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke yi bisa hadin gwiwarsu. Gwamnonin ...
Maza ku kiyayi kanku ku daina shan maganin karfin maza, a yau mutane 3 nasan sun sheka lahira saboda shan maganin karfin maza>>Inji Murja Kunya

Maza ku kiyayi kanku ku daina shan maganin karfin maza, a yau mutane 3 nasan sun sheka lahira saboda shan maganin karfin maza>>Inji Murja Kunya

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Murja Kunya ta jawo hankalin maza akan su daina shan maganin karfin maza inda tace yana kisa. Murja tace ko a yau mutane 3 tasan sun mutu dalilin shan maganin karfin maza. Murja tace mutum sai ya je ya asha maganin bashi da tabbas watakila matarsa sun yi fada ba zata bashi ba, a zo a samu matsala. https://www.tiktok.com/@murjess1/video/7520912629175438599?_t=ZM-8xaTYhDUijY&_r=1 Ikirarin Murja na maganin maza na kisa zai iya zama gaskiya dan kuwa akwai rahotanni da yawa akan hakan.
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda aka kai Amarya, Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Malika gidan Mijinta tana ta kuka

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda aka kai Amarya, Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Malika gidan Mijinta tana ta kuka

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wannan Bidiyon ya nuna yanda aka kai Amarya, Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Malika gidan mijinta, kuma abokin aikinta, Abdul M. Shareef. An ganta tana zubar da hawaye, kawaye na mata tsiya. Saidai wasu sun yi mamakin yanda take kukan Amarci ganin cewa, Bazawarace. https://www.tiktok.com/@sarauniyazully/video/7520748077519572280?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7520748077519572280&source=h5...
Kalli Bidiyo: Aiki Hajji Dai me Rabo, ba rikin Umarah bace da kowa ke iya zuwa>>Inji Garzali Miko bayan da ya dawo daga aikin Hajji

Kalli Bidiyo: Aiki Hajji Dai me Rabo, ba rikin Umarah bace da kowa ke iya zuwa>>Inji Garzali Miko bayan da ya dawo daga aikin Hajji

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa kuma mawaki, Garzali Miko ya dawo daga aikin Hajjin bana da aka yi dashi. Garzali Miko a filin jirgin sama an ga yanda akw hira dashi inda aka ce ya kara kyau, saidai yace ai ba ta yiyuwa mutum ya je aikin Hajji ya kara Kyau. Yace da dai Umarah ce da kowa ke iya zuwa amma aikin Hajji sai mai Rabo. https://www.tiktok.com/@kb_international/video/7520986097661316358?_t=ZM-8xaRSIccxdu&_r=1 Hakanan Garzali ya mayar da martani ga wanda yace masa ya jefi dan uwansa a wajan jifar Shedan inda yace shi dai yasan abinda yayi.