Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama masu laifin da suka tsere daga gidan gyara hali su 7, kalli Hotunansu ko kasan wani
Gwamnatin tarayya ta wallafa hotunan masu laifi da suka tsere daga gidan gyara hali na Ilesa dake jihar Osun.
Gwamnatin tace ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama su.
Da safiyar ranar Talata ne dai masu laifin suka tsere a yayin da ake tsaka da ruwan sama.








