‘Yan Bìndìgà sun yi gàrkuwà da babban Basarake a Arewacin Najeriya
Wasu ƴanbidga sun kai hari garin Okoloke da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma a jihar ta Kogi, inda suka kashe aƙalla mutum uku are da jikkata wasu da dama.
Maharan sun kuma yi garkuwa da babban basaraken al'ummar ta Okoloke, Pa Dada James Ogunyanda, a lokacin da ake tsaka da zaman fadanci, wanda bayanai suka tabbatar da cewa ba shi da cikakkiyar lafiya kuma yana daf da tafiya neman magani, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.
'Yan bindigar sun kuma kashe ƴanbanga biyu da wani ma'aikacin kamfanin sadarwa da ke aikin gyaran ƙarfen samar da sabis a yankin.
Rahotanni sun ce 'yan bangar na samar wa ma'aikacin sadarwar tsaro ne lokacin da maharan suka yi musu kwanton ɓauna inda suka buɗe musu wuta nan take.
Hare-haren 'yan bindiga dai na ci aba da ƙaruwa a baya-bayan n...








