Saturday, February 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ɓangaren Kwankwaso ba shi da hurumin korar mu daga NNPP saboda su ba halastattun shuwagabannin Jam’iyya bane- Kawu Sumaila

Ɓangaren Kwankwaso ba shi da hurumin korar mu daga NNPP saboda su ba halastattun shuwagabannin Jam’iyya bane- Kawu Sumaila

Duk Labarai
Ƴan majalisar dokokin Najeriya da jam'iyyar NNPP reshen jihar Kano ta dakatar sun yi watsi da matakin jam'iyyar, tare da bayyana ta a matsayin wadda "ba ta halasta ba". A yau Litinin ne shugaban jam'iyyar NNPP a jihar ta Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa ya sanar da dakatar da ƴan majalisar huɗu daga jam'iyyar bisa zargin su da ayyukan "zagon ƙasa". A a tattaunawarsa da BBC, Sanata Kawu Sumaila ya ce "ita kanta wannan jam'iyyar da waɗanda suka yi sanarwar, kotu tana cajin su da cewa su ba halastattun shugabannin jam'iyya ba ne, don haka ba su da iko ko damar ɗaukar wannan mataki." A game da batun gayyatar da shugaban jam'iyyar ta NNPP ya bayyana a lokacin sanar da dakatar da ƴan majalisar, Sumaila ya ce "gayyata ce kawai ta zumunci... shi ke nan yanzu jam'iyya sai ta hana ka gayyaci...
Uba Sani da Nuhu Ribadu ba abokaina ba ne yanzu – El-Rufa’i

Uba Sani da Nuhu Ribadu ba abokaina ba ne yanzu – El-Rufa’i

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya bayyana cewa 'a yanzu Uba Sani ba abokinsa ba ne' bayan abubuwan da ke faruwa baya-bayan nan. El-Rufa'i ya bayyana hakan ne a tattaunawar da ya gudanar da tashar talabijin ta Arise da yammacin yau Litinin. Bayan kammala wa'adinsa na shekara takwas a matsayin gwamnan jihar Kaduna, tsohon gwamnan na fuskantar bincike kan kuɗaɗe da ake zargin sun yi ɓatan-dabo a lokacin mulkinsa. Lamarin ya haifar da muhawara kasancewar thonon gwamnan na Kaduna, Nasir El-Rufa'i da gwamna mai ci Uba Sani sun kasance masu kusanci a tsawon shekara takwas na mulkin tsohon gwamnan. El-Rufa'i ya bayyana cewa aboki shi ne mutumin da zai kawo maka ɗauki ko a lokacin daɗi ko na tsanani. Ya ce "a yanzu Uba Sani da Nuhu Ribadu ba abokaina ba ne. "Na san c...
Majalisa bata ki tantanceni ba, Tinubu ne ya fasa bani mukamin Minista>>El-Rufai

Majalisa bata ki tantanceni ba, Tinubu ne ya fasa bani mukamin Minista>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamna jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa majalisar tarayya bata ki amincewa dashi ba a matsayin minista. Yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne ya fasa bashi mukamin na minista. El-Rufai ya bayyana hakanne a yayin ganawar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Maganar nada El-Rufai Minista dai itace abinda ta jawo har aka samu tsamin dangantaka tsakanin El-Rufai da gwamnatin Tinubu.
Da Duminsa: NNPP ta Dakatar da Sen. Kawu Sumaila, Ali Madakin Gini, Kabiru Alhassan Rurum da Abdullahi Sani Rogo daga jam’iyyar

Da Duminsa: NNPP ta Dakatar da Sen. Kawu Sumaila, Ali Madakin Gini, Kabiru Alhassan Rurum da Abdullahi Sani Rogo daga jam’iyyar

Duk Labarai
YANZU-YANZU: NNPP A Kano Ta Dakatar Da Kawu Sumaila Da Rurum Da Ali Madaki Jam'iyyar NNPP a jihar Kano ta dauki matakin ladabtarwa kan wasu mambobinta, ciki har da sanata da 'yan majalisar dokoki, bisa zargin aikata ayyukan da suka sabawa manufofin jam'iyyar. Shugaban jam'iyyar na jihar, Alhaji Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano ranar Litinin. Ya ce, daga cikin 'yan majalisar da abin ya shafa akwai Sanata Kawu Sumaila mai wakiltar Kano ta Kudu, Alhaji Abdullahi Sani Rogo, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Rogo, Alhassan Rurum mai wakiltar Rano/Kibiya, da kuma Ali Madakin Gini mai wakiltar mazabar Dala a majalisar wakilai. Shugaban jam'iyyar ya bayyana cewa, jam'iyyar ta nuna rashin jin dadinta kan halayen wasu daga cikin 'yan majalisar tara...
Shaida ya gayawa kotu cewa Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello bashi da hannu a maganar siyan gidan Naira Miliyan dari biyar

Shaida ya gayawa kotu cewa Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello bashi da hannu a maganar siyan gidan Naira Miliyan dari biyar

Duk Labarai
Shaida ya gayawa kotun tarayya dake Abuja cewa, Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello bashi da hannu game da maganar sayen gidan Naira Miliyan 550 a Maitama Abuja. Sannan an gayawa kotun cewa, duka takardun sayen gidan basu dauke da sunan Tsohon Gwamnan. Shaidan da ya bayar da wannan bayani na hukumar EFCC ne. Shaidan EFCC me suna Olusegun Joseph Adeleke wanda dillalin gidajene lauyan EFCC Kemi Pinheiro, SAN ne ya kawoshi. Shaidan yace shugaban kamfaninsu, Fabian Nwora ne ya kirashi suka yi zaman tattaunawa da wanda zai sayi gidan na Naira Miliyan 550 me suna Shehu Bello. An tambayeshi yayin cinikin ko ya ga Tsohon Gwamnan jihar Kogin inda yace bai ganshi ba. Saidai yace bayan an kammala ciniki, Shehu Bello ya biya kudin gida, daga baya ya koma inda ya nemi a bashi kudin...
Mun gano cewa El-Rufai na kokarin Tadewa Tinubu kafa ya hanashi zarcewa a 2027, saidai abin da ke mana dadi ‘yan Arewa basu tare ashi>>APC

Mun gano cewa El-Rufai na kokarin Tadewa Tinubu kafa ya hanashi zarcewa a 2027, saidai abin da ke mana dadi ‘yan Arewa basu tare ashi>>APC

Duk Labarai
Jam'iyyar APC ta mayar da martani akan maganganu da avubuwan da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke yi. Kakakin APC, Ajibola Basiru ne ya bayyana hakan a wata ganawa da yayi da manema labarai inda yace abinda ke damun El-Rufai shine da bai samu ya zama minista a Gwamnatin Tinubu ba. Yace daga nan ne sai El-Rufai ya koma sukar Gwamnatin Tinubun, yace amma abinda ke musu dadi shine a Arewar ma shi ba wani me fada aji bane. Ya kara da cewa, El-Rufai na ta kokari ne kawai yaga ya kawo tarzoma da raba kai tsakanin Arewa da kudu, ta wannan hanyar ne yake son yin suna. Tsohon Gwamnan na Kaduna dai sunansa ya fito a cikin mutanen da Tinubu yaso ya nada a matsayin ministoci amma da yaje majalisa sai ya kasa tsallake tantancewar da aka yi kokarin yi masa. bayan ...

Akwai yiyuwar fadawa matsalar karancin man fetur a Najeriya saboda masu dakon man sun fusata sun daina dauka

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, akwai yiyuwar Najeriya ta fada matsalar karancin man fetur saboda masu dakon man fetur din sun dakata da dakonsa. Direbobi masu dakon man fetur din sun dakata da dakon man ne saboda zargin cin zarafinsu da ake yi da sukawa hukumar gwamnatin jihar Legas da ma'aikatar sufuri ta tarayya. Hakanan suma masu kamfanonin sadarwa sun yi gargadin cewa, za'a iya samun matsalar sabis idan direbobin dakon man suka daina daukar man saboda dashi suke amfani wajan gudanar da ayyukansu. Jaridar Punchng ta bayyana cewa a ranar Asabar da Lahadi da suka gabata direbobin man sun ki daukar man fetur din. Shugaban kungiyar direbobi ta NARTO Yusuf Othman ya bayyana cewa wannan lamari yayi kamari dan kuwa mahukuntan jihar Legas na kama musu motoci suna tafiya dasu ofis, suna...
An kama magidanci da ya Kkàshè matarsa

An kama magidanci da ya Kkàshè matarsa

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Edo sun kama wani magidanci me sunan Kelvin Izekor bisa zargin kashe matarsa. Makwabtansu sun bayyana cewa, Kelvin da matarsa, Success Izekor basu dade da yin aure. Bidiyon lamarin da ya faru ya karade shafukan sada zumunta inda aka ga 'yansanda sun dauke gawar matar da sarar adda akanta. Kakakin 'yansandan jihar, Moses Yamu ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace mafusatan matasa sun so kashe mijin amma zuwan 'yansanda suka yi nasarar kubutar dashi. Yace sun tafi da mijin dan gudanar da bincike inda yace sun kai matar Asibiti inda likita ya tabbatar da cewa ta mutu. Yace duk wanda aka samu da laifi za'a hukuntashi.
Ba’a isa a hanamu yin hukunci da shari’ar musukunci ba>>Musulman Yarbawa suka mayarwa da Gwamnoninsu Martani

Ba’a isa a hanamu yin hukunci da shari’ar musukunci ba>>Musulman Yarbawa suka mayarwa da Gwamnoninsu Martani

Duk Labarai
Shugaban kotun shari'ar Musulunci dake jihar Kwara, Justice Abdurraheem Sayi ya bayyana cew basa bukatar amincewar hukumin Gwamnati ko na sarakunan gargajiya kamin su kafa kotun shari'ar Musulunci. Yace duk masu adawa da kafa kotunan shari'ar musulunci a jihohin Yarbawa kiyayyar addinin ce kawai ta sasu hakan ba wani abuba. Ya bayyana hakane a yayin da yake gabatar da yawabi a jami'ar Legas akan maganar shari'ar Musulunci a jihohin Yarbawa. Ya bayyana cewa ko shugaban kasa, doka bata bashi damar hana samar da kotun shari'ar Musulunci ba. Yayi kira ga mahukunta a yankin dasu bayar da dama ga musulman dake so su aiwatar da shari'ar Musulunci domin dokokin jihohinsu basu baiwa musulmai irin wannan dama ba.