Sunday, July 12
Shadow

Author: Bashir Ahmed

El-Rufai da Peter Obi Sun Tattauna a Gefen Taron Cambridge Africa Together a Birtaniya

El-Rufai da Peter Obi Sun Tattauna a Gefen Taron Cambridge Africa Together a Birtaniya

Duk Labarai
YANZU-YANZU: El-Rufai da Peter Obi Sun Tattauna a Gefen Taron Cambridge Africa Together a Birtaniya. An hango tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, na tattaunawa da ɗan takarar Shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Mista Peter Obi, a gefen taron shekara-shekara karo na 11 na Cambridge Africa Together Conference (ATC), wanda ke gudana a Jami’ar Cambridge, ƙasar Birtaniya. Taron, wanda ke ɗaya daga cikin manyan taruka da ke haɗa shugabanni, masana da matasa daga sassa daban-daban na nahiyar Afirka da duniya, ya kasance dandali na musayar ra’ayoyi, tattaunawa kan ci gaban Afirka, shugabanci da sabbin dabaru na magance matsalolin da ke fuskantar nahiyar. El-Rufai da Peter Obi, wadanda dukkansu sanannu ne a harkar siyasar Najeriya, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen ...
Gwamnonin Arewa na taro kan matsalar tsaro a Kaduna

Gwamnonin Arewa na taro kan matsalar tsaro a Kaduna

Duk Labarai
Gwamnonin arewa da kuma sarakunan gargajiya na gudanar da taro a Kaduna, domin tattaunawa kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankin. Taron wanda ke gudana a gidan gwamnatin jihar ta Kaduna, zai kuma tattauna kan matsalar talauci da yaran da ba su zuwa makaranta da kuma sauran al'amura da suke damun yankin. Gwamnonin jihohin Zamfara da Kebbi da Gombe da Neja da kuma Zamfara na cikin waɗanda ke halartar taron. A ɓangaren sarakunan gargajiya kuma akwai mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III da Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da Etsu na Nupe da Sarkin Zamfara da Sarkin Bauchi da Sarkin Ilorin da Sarkin Keffi da sauransu.
Haziƙin Matashi Ya Kammala Digirinsa Da Sakamako Mafi Kyau A Bangaren Kimiyya A Jami’ar Aliko Dangote Dake Wudil

Haziƙin Matashi Ya Kammala Digirinsa Da Sakamako Mafi Kyau A Bangaren Kimiyya A Jami’ar Aliko Dangote Dake Wudil

Duk Labarai
Haziƙin Matashi Ya Kammala Digirinsa Da Sakamako Mafi Kyau A Bangaren Kimiyya A Jami'ar Aliko Dangote Dake Wudil Muhammad Abubakar Ɗan Haya kenan dalibin da ya zama gwarzo a bangon karatu na shekarar 21/22, inda ya fita da sakamako mafi daraja a fannin kimiyya (Engineering) jami'ar Aliko Dangote dake Wudil. Abubakar ɗan Haya, ya fito daga ƙaramar hukumar Birnin-Kudu dake jihar Jigawa. Daga Abubakar Shehu Dokoki
Hajj 2025: Maniyyata fiye da 2000 sun tashi zuwa ƙasa mai tsarki

Hajj 2025: Maniyyata fiye da 2000 sun tashi zuwa ƙasa mai tsarki

Duk Labarai
Hukumar alhazan Najeriya ta ce ya zuwa ranar misalin ƙarfe 8:02 ta yi jigilar maniyyata 2,006 zuwa ƙasa mai tsarki. Hukumar ta bayyana a shafinta na X cewa jirgin MaxAir ya tashi daga birnin Bauchi zuwa Madina, inda ya kwashi maniyyata 384 da kuma jami'i guda ɗaya. Wannan dai shi ne cikamakin jirgi na biyar da suka yi jigilar maniyyatan daga ranar da aka ƙaddamar da jigilar wato ranar Juma'a.
Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne – Kwankwaso

Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne – Kwankwaso

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kano, sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya soki ƴan siyasar da ke sauya sheƙa bayan sun gama cin moriyar jam'iyyar, abin da ya bayyana da babban kuskure a siyasance. Sanata Kwankwaso wanda ya bayyana hakan a Kano lokacin da yake karɓar wasu ƴan siyasar da suka sauya sheƙa zuwa NNPP daga ƙaramar hukumar Takai, a gidansa da ke Miller road a birnin Kano. A baya-bayan nan ne dai raɗe-raɗi suka yi ta yawo cewa Kwankwason zai koma jam'iyya mai mulki ta APC. Rabi'u Kwankwaso ya ƙara jaddada irin juriya da haɗin kai da ke tafiyar Kwankwasiyya duk kuwa da cewa an ta ƙoƙarin ganin an kawar da hankalin mabiya.