Wannan ɗaya dagga cikin wa "yanda suka rasa rayukansu a harin "yan bindiga a jiya da misalin karfe 5pm AGARIN BURMUKAI, DANGULBI, MARU, ZAMFARA STATE OF NIGERIA
Mai martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Farouk ya bayyana cewa ba domin kuɗi Masarautar ke nade-naden sarauta ba, suna yi ne domin neman Aljannah.
An jiyo Sarkin ya bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen yada labarai, ya yin da masarautar ke naɗa wani muƙami. Mene ne ra'ayoyin ku?
Me za ku ce?
Kungiyar dake ikirarin jìhàdì ta Ansaru ta je kusa da babban birnin tarayya Abuja ta kafa sansani.
Rahoton yace kungiyar wadda ta balle daga Bòkò Hàràm ta kuma kafa sansanoni 8 a cikin jihar Kogi.
Wasu daga cikin sansanonin kungiyar na tsakanin Obajana da Kabba wanda hakan yasa manyan mutane dake wucewa ta wajan biyan kudi masu yawa dan samarwa kansu tsaro yayin wucewa ta wajan.
Rahoton yace babban wajan horas da 'yan kungiyar na kilomita 93 ne tsakaninsa da babban birnin tarayya, Abuja.
Kokarin jinn ta bakin hukumomin tsaro kan lamarin ya ci tura.
Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya bayyanawa ma'aikatun wutar Lantarki na kasa cewa Gwamnati ba zata sake amincewa da rashin samar da wutar lantarkin ba.
Ya bayyana hakane bayan amincewa da sabon daftarin gyaran wutar.
Yace kuma an samar da wani sabon tsari na baiwa ma'aikatan wutar Lantarkin horaswa ta musamman. Inda yace nan da shekaru 10 za'a magance matsalar karancin ma'aikata a hukumar wutar lantarkin.
Raɗe-raɗin dawowar Kwankwaso jam'iyyar APC mai mulki, na cigaba da fitowa fili.
An samu rudani a sakateriyar jam’iyyar APC, a ranar Talata, bayan da Shugaban jam’iyyar na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Jiha na Harkokin Gidaje da Ci gaban Birane, Yusuf Ata, suka yi sabani kan daowawar Kwankwaso jam'iyyar APC.
Yayin da Minista Ata ke cewa Kwankwaso – wanda kuma tsohon Ministan Tsaro ne – ya rasa karbuwa a Kano kuma siyasar sa na dab da mutuwa, Ganduje ya ce APC ba lallai ta ki karbansa ba, yana mai cewa “aboki a lokacin bukata, aboki ne na gaskiya.”
Ata, yayin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawa da Ganduje a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, ya bayyana cewa matsin lambar siyasar da Kwankwaso ke ciki ne ke sa shi kokarin dawowa APC, yana mai cewa har Kw...
Tauraron mawakin Hausa, Dauda Kahutu Rarara ya kuma dauki hotuna da uwargidansa bayan na amarya, A'isha Humaira da suka karade kafafen sadarwa.
https://www.tiktok.com/@mrsrarara/video/7501307799503146245?_t=ZM-8w9HQQia779&_r=1
An ga Rarara da Uwargidansa suna buga soyayya a hotunan da ya saki.
Mutane Sama da 210 tare da ya'yansu Sun karbi Addinin Muslunci.
Fiye da mutum 210 tareda ‘ya’yansu ne suka Karbi Addinin musulinci a kauyen (Jadebri) da ke karamar hukumar (Bandai) a Arewacin Ghana.
Allah ya ɗaukaka Addinin Muslunci da Musulmai Sannan Ana Bukatar Kayi Sharing Zuwa group group domin Samun Addu'o'in Al'ummar Musulmai Allah ya Dawwamar dasu a Cikin Addinin Muslunci
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Biyawa Halisa Muhd Naira Miliyan 15 Don Ci Gaba da Maganin Cututtukan da ke Damunta
Mai girma Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake nuna jajircewarsa wajen tallafawa marasa lafiya masu bukata ta musamman, inda ya biya Naira miliyan 15 domin ci gaba da maganin Halisa Muhd, wadda ke fama da cutar daji (cancer).
Wannan kudin na daga cikin tallafin da Gwamnan ya bayar domin taimakawa Halisa Muhd wajen samun magani mai tsada, bayan da ya riga ya biya kudin aikin farko da aka yi mata.
Fauziyya D. Sulaiman, Babbar Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Mabukata da Gajiyayyu, ta bayyana godiyarta ga Gwamnan bisa wannan taimako, tare da jaddada cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da tallafawa marasa lafiya da masu bukata ta musamman a jihar.
Wannan ...
Madugun Adawar Siyasa A Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma ba shi da niyyar ficewa daga cikinta. Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da mata mambobin Kwamitin Amintattu na jam’iyyar (BoT) da suka kai masa ziyara domin neman hanyoyin ceto jam’iyyar daga rushewa gaba daya.
A cewar Atiku, rahotannin da ke cewa yana shirin barin PDP zuwa wata jam’iyya kamar SDP ba su da tushe balle makama, kuma an kirkire su ne domin rikita shirin kafa kawancen jam’iyyun adawa da ake yi. Ya jaddada cewa yana nan a matsayin cikakken memba na PDP, kuma yana jagorantar yunkurin kafa kawancen jam’iyyun adawa domin kalubalantar jam’iyyar APC a zaben 2027.
A wata ganawa da aka yi a Abuja, Atiku y...
Majalisar wakilai ta bayyana cewa alamu na kara fitowa fili dake nuna mayakan Kungiyar Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau.
Majalisar ta bayyana hakane a zamanta na ranar Talata inda ta bayyana damuwa matuka kan harin da ake zargin kungiyar ta Boko Hàràm da kaiwa a barikin sojoji ta Giwa dake jihar Borno.
Majalisar tace wannan alamace karara dake nuna cewa mayakan kungiyar ta Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau.
'yan majalisar sun kuma bayyana damuwa kan yanda kungiyar ke dawowa a hankali da kuma asarar rayukan da ake samu a hare-haren da take kaiwa a jihohin Borno da Yobe.
Duk da yawan kudin da gwamnati ke warewa bangaren tsaro na karuwa duk shekara, amma korafi na yawa a kan yawa ko ingancin makaman da ake siyowa sojojin.
Misali a shekarar...