Thursday, February 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Babbar Kotun Birnin Tarayya da ke Kuje ta dage gurfanar da tsohon Sakataren NHIS, Farfesa Usman Yusuf, zuwa ranar 3 ga Fabrairu, 2025

Babbar Kotun Birnin Tarayya da ke Kuje ta dage gurfanar da tsohon Sakataren NHIS, Farfesa Usman Yusuf, zuwa ranar 3 ga Fabrairu, 2025

Duk Labarai
EFCC ta kama Yusuf bisa zargin aikata almundahana kuma an shirya gurfanar da shi a ranar 30 ga Janairu, amma kotu ta jinkirta shari'ar don bai wa masu gabatar da kara damar gyara tuhume-tuhumen da ke kansa. An ki amincewa da bukatar Bada beli, inda alkalin kotu ya umarci a ci gaba da tsare shi a hannun EFCC har zuwa ranar da za a sake gurfanar da shi. Menene ra'ayinku?
Bata gari sun sake kaiwa wutar lantarkin Najeriya hari

Bata gari sun sake kaiwa wutar lantarkin Najeriya hari

Duk Labarai
Rahotanni daga kamfanin kula da wuta na kasa, TCN sun bayyana cewa, wasu bata gari sun sake kaiwa wutar lantarkin Najeriya hari. Rahoton yace an kaiwa Tangarahon wutar ne dake kan titin Ugwuaji zuwa Makurdi a jihar Benue hari. Me kula da yada labarai ta kamfanin, Ndidi Mbah ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba. Tace an yi barnar ne a ranar Asabar, 25 ga watan Janairu na shekarar 2025. Tace da misalin karfe 3 na darene aka kai harin saidai mazauna garin sun ankara da maharan kamin su aikata wannan barna inda suka kai musu wawa, an kama mutum daya inda sauran suka tsere. Sun mika wanda suka kama din ga 'yansanda kamar yanda Mbah ta bayyana. Tace suna yabawa mutanen kauyen na Watuolo bisa wannan kokari inda ta yi kira ga sauran garuruwan da irin wad...
YANZU-YANZU: An Baiwa Hammata Iska A Taron Kwamitin Amintattu Na Jam’iyyar PDP

YANZU-YANZU: An Baiwa Hammata Iska A Taron Kwamitin Amintattu Na Jam’iyyar PDP

Duk Labarai
Daga Comr Nura Siniya Rikici ya kunno kai a babbar Hedikwatar jam’iyyar PDP, ta kasa inda ake gudanar da taron kwamitin amintattu (BoT) na jam'iyar, a lokacin da aka yi yunkurin hana wani jigo a jam’iyyar Sunday Ude-Okoye, shiga wajen taron Rikicin ya kunno kai a daidai lokacin da tsakanin Samuel Anyanwu da Ude-Okoye, su ke neman zama sakataren jam’iyyar na kasa.
Fasinjoji sun tsallake rijiya da baya yayin da jirgin Max Air yayi Hadari a Kano

Fasinjoji sun tsallake rijiya da baya yayin da jirgin Max Air yayi Hadari a Kano

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Jirgin Max Air ya tunkuyi ƙasa wajen sauƙa a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano Jigin saman Max Air ƙirar Boeing 737 wanda ya dauko fasinjoji daga Lagos zuwa Kano ya tunkuyi ƙasa wajen sauƙa a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano a daren Talatan nan. Ganau sun ce dirar jirgin ke da wuya tayar gaba ta fashe, kuma ta kama da wuta. Daga nan sai jirjin ya yi taga-taga, goshinsa ya tunkuyi ƙasa. Tuni dai ma’aikatan kwana-kwana su ka daƙile faruwar gobara a jirgin, kuma fas...
YANZU-YANZU :Hussaina matar Seaman Abbas ta ce yanzu basa tare da mijinta Seaman Abbas

YANZU-YANZU :Hussaina matar Seaman Abbas ta ce yanzu basa tare da mijinta Seaman Abbas

Duk Labarai
Ba sakinta ya yi ba amma wulakanci da hantara da cin mutuncin da take zargin yake mata shi da danginsa da yan garinsu abun yayi yawa, kuma duk suna yi mata cin mutuncin ne saboda zargin an bata gudunmawar Naira milyan N20 daga Berekete Family. Tace kuma ba gaskiya bane ba a bata ko sisi ba. Yanzu dai haka bayan sun fatattako ta daga gidan mijin tana cen tana fama da rashin lafiya har ma ta roki a taya ta da addu'a… Abun lura shine Seaman Abbas ya ji sauki, yana cikin hayyacinsa, ya dawo lafiyarsa lau
Kungiyoyin kare hakkin masu amfani da wayoyin hannu sun maka Gwamnati a kotu saboda karin kudin kiran waya da kaso 50

Kungiyoyin kare hakkin masu amfani da wayoyin hannu sun maka Gwamnati a kotu saboda karin kudin kiran waya da kaso 50

Duk Labarai
Kungiyoyin dake fafutuka dan kare hakkin masu amfani da wayar hannu aun mikawa hukumar kula da sadarwa ta kasa NCC korafin rashin amincewarsu kan karin kudin kiran waya da kaso 50 cikin 100. Sun mika korafinne nan ranar Juma'ar data gabata inda suka bukaci a basu amsa nan da ranar Talata ko su shiga kotu. Kamfanonin sadarwa sun nemi a basu damar kara kudin kiran waya da kaso 100 bisa dari watau su nunka amma NCC ta basu damar kara kaso 50 cikin 100. Wannan kari dai shine irinsa na farko a cikin kusan shekaru 10 da suka gabata. Kungiyar NATCOMS na daga cikin kungiyoyin da suka shigar da wannan korafi, kuma shugabanta, Adeolu Ogunbanjo, ya shaidawa jaridar Punchng cewa, tunda har ranar Talata basu ji amsa ba daga NCC, to basu da zabin da ya wuce su shiga kotu. Jaridar ta yi ko...
Ba zan bar Jam’iyyar APC ba>>El-Rufai

Ba zan bar Jam’iyyar APC ba>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ba zai bar Jam'iyyar APC ba. El-Rufai ya bayyana hakane a wata ganawa da yayi da 'yan Jarida ranar Talata a Abuja wajan taron karfafa Dimokradiyya a Najeriya. Yace ba zai bar Jam'iyyar APC ba. An tambayeshi to me yasa yake sukar Jam'iyyar APC din sai yace ai yana so su gyara ne kuma yana tsammanin zasu gyara din. Daga nan ya wuce abinsa.
El-Rufai na son kifar da Gwamnatin mu>>Inji Gwamnatin Tarayya

El-Rufai na son kifar da Gwamnatin mu>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnatin tarayya ta yi martani akan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda tace a baya yana tare da ita amma yanzu yana son kifar da gwamnatin. Hakan na zuwane bayan da Tsohon Gwamnan yayi tsokaci akan gwamnatin Tinubu inda yace Jam'iyyar APC ta kaucewa tubalin da aka dasata akai na shugabanci me kyau. Me baiwa shugaban kasa shawara na musamman akan sadarwa, Daniel Bwala ya mayar da martanin ta shafinsa na kafar X inda yace da El-Rufai na cikin gwamnatin ...
Jahilaine ke shugabantar Najeriya a yanzu>>Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Jahilaine ke shugabantar Najeriya a yanzu>>Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, Jahilaine ke mulkar Najeriya a yanzu inda yace yawanci wanda basu da isashshen limi ko Wanda basu dashine suke gaba-gaba a Gwamnati. El-Rufai ya bayyana hakane a wajan wani taron karfafa Dimokradiyya da ya faru a babban barnin tarayya, Abuja. El-Rufai ya zargi Jam'iyyar APC da yin halin ko in kula game da yin shugabanci na gari. El-Rufai yace shi bai ganewa kan Jam'iyyar APC ba dan kuwa komai nata ya lalace ba taron Jam'iyyar babu wata harka ta ci gaba.