Najeriya ta lalace, sai an sha wuya kamin ta dawo daidai>>Kashim Shettima
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, Najeriya ta samu matsalar rashin kula a baya dan haka gyaranta sai an sha wuya.
Ya bayyana hakane ta bakin wakilinsa, Hakim Baba Ahmad a yayin da ya wakilceshi zuwa taron karfafa Dimokradiyya a Abuja jiya.
Ya kara da cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana sane da irin halin matsin rayuwa da al'ummar Najeriya ke ciki kuma zai dauki matakin gyara a inda ya kamata.
Ya kara da cewa, Gwamnatinsu da Bola Ahmad Tinubu ke jagoranta zata ci gaba da yaki da rashawa da cin hanci da tada komadar tattalin arziki da ci gaba da goyon bayan zaben gaskiya.








