Thursday, February 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ana zargin DPO da yin lalata da karamar yarinya me shekaru 15 da aka tsare a fishin ‘yansanda a Katsina

Ana zargin DPO da yin lalata da karamar yarinya me shekaru 15 da aka tsare a fishin ‘yansanda a Katsina

Duk Labarai
Ana zargin DPO din 'yansanda dake Dutsinma, CSP Bello Gusau da yiwa karamar yarinya lalata wadda ake tsare da ita a ofishin 'yansanda. Wata kungiyar kare hakkin bil'adama HRTI ce shigewa yarinyar gaba inda suke nema mata hakkinta. Shugaban kungiyar Kwamared Maiyasin ya bayyana cewa sai da suka yi bincike suka tabbatar da cewa DPO din ya dauki yarinyar ya je ya kwana da ita a gidansa, ba'a ofishin 'yansanda ta kwana ba kamin su dauki mataki. Kwamishinan 'yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Musa ya bayyana cewa an dakatar da DPO din inda aka fara bincike kan lamarin.
Ba zamu iya ci gaba da biyan tallafin wutar Lantarki ba>>Gwamnatin Tarayya

Ba zamu iya ci gaba da biyan tallafin wutar Lantarki ba>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Shugaban kwamitin dake kula da yanda Gwamnatin tarayya ke kashe kudi, James Faleke ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ba zata iya ci gaba da biyan kudij tallafin wutar lantarki ba. Ya bayyana hakane yayin da ma'aikatar kudi ke bayanin yanda zata kashe kudadenta a shekarar 2025. Gwamnatin tarayya dai ta ware Naira biliyan 705 dan biyawa 'yan Najeriya tallafin wutar a shekarar 2025. Saidai Falake yace sam babu bukatar hakan musamman lura da yanda farashin wutar labtarkin ke ta kara tashi kullun da kuma yanda darajar Naira ke ci gaba da faduwa.
An kama wannan tsagerar da ta sha Alwashin zin lalata da maza 100 a rana daya

An kama wannan tsagerar da ta sha Alwashin zin lalata da maza 100 a rana daya

Duk Labarai
Hukumomi a kasar Turkiyya sun kama wata tsagera data yi suna wajan nuna tsiraici me suna Ezra Vandan 'yar shekaru 23 saboda Alwashin da ta sha na yin lalata da maza 100 a cikin awanni 24. 'Yansanda a birnin Istanbul sun kama matar ne bisa zargin cewa abinda take da niyyar aikatawa ya sabawa al'adar kasar kuma zai jawo gurbacewar tarbiyya. Matar dai ta yi aniyar daukar bidiyon lalatar da zata yi kai tsaye tare da nunawa Duniya. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da wata tsagerar me suna Brit Bonnie Blue ta yi ikirarin yin lalata da maza guda 1000 a rana daya.
Bamu yadda da karin kudin kiran waya ba, muna kiran ‘yan Najeriya su kauracewa kamfanonin sadarwa>>NLC

Bamu yadda da karin kudin kiran waya ba, muna kiran ‘yan Najeriya su kauracewa kamfanonin sadarwa>>NLC

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago NLC ta bayyana cewa, bata yadda da karin kudin kiran waya na kamfanonin sadarwa ba da aka yi zuwa kaso 50 cikin 100. Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana haka ranar Laraba ga manema labarai inda yace hakan ya zo ne a lokacin da ake fama da tsadar rayuwa gashi kuma babu kudin sayen kayan masarufi. Joe Ajaero yace amfani da kafafen sadarwa ya zamarwa 'yan Najeriya dole ta yanda suke kashe akalla kaso 10 cikin 100 na kudin shigarsu akan harkar sadarwa. Joe Ajaero yace kungiyar kwadago ta yi Allah wadai da wannan lamari inda yace basu amince dashi ba.
Komai Nawa ya koma na mata, duk me kokwanto ya zo in nuna masa>>Inji Dan Daudu Bobrisky bayan da shugaban Amurka, Donald Trump ya haramta Luwadi

Komai Nawa ya koma na mata, duk me kokwanto ya zo in nuna masa>>Inji Dan Daudu Bobrisky bayan da shugaban Amurka, Donald Trump ya haramta Luwadi

Duk Labarai
Shahararren me shigar mata da daudanci a Najeriya wanda aka fi sani da Bobrisky ya yi magana bayan da shugaban kasar Amurka ya haramta luwadi da Madigo. Bobrisky yayi suna sosai wajan daudanci inda har a karshe yace ya bar Najeriya da zama saboda takurawar da aka masa. A ranar da aka rantsar dashi a matsayin shugaban kasar Amurka a karo na 2, Donald Trump ya bayyana cewa, jinsin maza da mata kawai suka sani a Amurka. A rubutun da yayi a shafinsa na sada zumunta, Bobrisky ya bayyana cewa, Ya ji ance shugaban Amurka, Donald Trump yace maza da mata kawai ya sani, amma shi gashi ya koma mace, yace idan ana so, zai bude aga hujja.
Za’a samu saukin rayuwa, kayan masarufi zasu sauka kasa>>Inji Gwamnatim tarayya

Za’a samu saukin rayuwa, kayan masarufi zasu sauka kasa>>Inji Gwamnatim tarayya

Duk Labarai
Ministan kudi da tattalin arziki, Wale Edun ya bayyana cewa a shekarar 2025 za'a samu saukin hauhawar farashin kayan masarufi. Yace alkaluman hauhawar farashin kayan masarufi zasu yi kasa zuwa kaso akalla 15 cikin 100 inda a yanzu suke a maki 34.8 kamar yanda hukumar kididdiga ta kasa, NBS ta bayyana. Ya bayyana hakane a Abuja ranar Litinin yayin kaddamar da kwamitin kula da kudi inda yace zasu cimma burin samun kudin shiga na Naira Tiriliyan 47.9 da suka saka a gaba a shekarar 2025. Yace babban bankin Najeriya, CBN ya saka burin rage hauhawar farashin kayan abinci zuwa kaso 15 cikin 100 a cikin shekarar nan kuma zasu dage dan cimma wannan buri.
Kalli Bidiyo: An hango me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg na kallon Nonuwan matar me kamfanin Amazon a wajan taron rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban kasa

Kalli Bidiyo: An hango me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg na kallon Nonuwan matar me kamfanin Amazon a wajan taron rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban kasa

Duk Labarai
Abinda me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg yayi a wajan rantsar da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya dauki hankula. Bidiyo ya nuna Mark Zuckerberg yana kallon nonuwan matar me kamfanin Amazon, watau Jeff Bezos. Lamarin ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke ganin itama bai kamata ta yi irin wannan shigar ta nuna kirji ba a wajan taro me muhimmanci irin wannan ba. https://www.tiktok.com/@musicedits304/video/7462128836424092946?_t=ZM-8tFH4LH9YBh&_r=1 Kalli Bidiyin anan Manyan masu kudin Duniya da suka mallaki kamfanonin sadarwa dana kasuwanci irin su Facebook, Amazon, Tiktok, Apple da saransu duk sun halarci wajan taron rantsar da Donald Trump.
Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47

Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47

Duk Labarai
Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47, bayan nasarar da ya yi a zaɓen shugaban ƙasar na 2024. An rantsar da Donald Trump ne a cikin ginin Majalisar Dokokin ƙasar na Capitol, karon farko a cikin shekaru. Gabanin Trump, an rantsar da mataimakinsa, kuma tsohon mai sukarsa, JD Vance. Jim kaɗan bayan shan ranstuwa, Trump ya sanar da wasu tsauraran matakai da zai ɗauka, musamman a ɓangaren tsaron iyaka da kuma rage kwararar baƙi zuwa ƙasar. Wani abin kuma shi ne yadda Trump ya riƙa sukar magabacinsa, Joe Biden, a gabansa, jim kaɗan bayan shan rantsuwa. Donald Trump ya dawo kan mulki ne bisa alƙawarin kawo tsauraran sauye-sauye waɗanda suka sha bamban da na Biden. A jawabinsa na farko, Trump ya ce ''Sabon babin ci gaban Amurka zai fara ne daga yau''. '...

Maganin warin baki

Magunguna
Idan ana son yin maganin warin baki ga hanyoyin da masana kiwon lafiyar baki suka bayar da shawarar ya kamata a bi dan samun nasara. A rika wanke baki da goge harshe duk bayan an kammala cin abinci, akwai abin goge harshe na musamman da ake sayarwa, kuma da yawa burushin goge baki ana yinsa ta yanda mutum zai iya amfani dashi wajan goge harshe amma mutane da yawa basu sani ba. Ka duba bayan burushin goge bakinka, idan kaga yana da kurzuni-kurzuni ko kaushi to alamace zaka iya juya bayan ka goge harshenka dashi duk bayan kammala cin abinci. Hakanan masana kiwon lafiyar baki da hakora sun bada shawarar rika yin sakace ana cire abinci da ya makale a tsakanin hakora duk bayan kammala cin abinci dan kawar da warin baki. Hakanan ana son mutum ya rika canja burushin wanke baki akai-ak...
Coci a jihar Delta ta kori Reverend Fr. Daniel Okanatotor saboda ya je kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci bashi ba aure tunda ya kai mukamin Priest

Coci a jihar Delta ta kori Reverend Fr. Daniel Okanatotor saboda ya je kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci bashi ba aure tunda ya kai mukamin Priest

Duk Labarai
Coci a jihar Delta ta dakatar da Fr. Daniel Okanatotor saboda zuwa kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci tunda ya kai matsayin Priest, to bashi ba aure har ya mutu. Cocin me suna The Catholic Diocese of Warri ta sanar da cewa ta dakatar da Fr. Daniel daga mukamin Priest a wata sanarwa data fitar ranar 16 ga watan Janairu Tace Fr. Daniel ya sanar da ita cewa zai ajiye mukamin na Priest, saidai tace kamin ta kammala sauke masa mukamin, sai kawai ta ji labarin yayi aure. Dan haka ne ta sanar da dakatar dashi.